• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukuma Ta Koka Da Yadda Masu Mulki Ke Tauye Hakkin Al’umma

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai, Makala
0
Hukuma Ta Koka Da Yadda Masu Mulki Ke Tauye Hakkin Al’umma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kare hakkin Bil’adama ta kasa (NHRC) ta ce ta amshi koke san cin zaraf-in take hakkin Bil’adama har guda 55,218 a watan Mayu da tattaro a jihohin da suke fadin Nijeriya, manyan korafe-korafe an samesu ne a kan masu madafun iko da suke jihohi daban-daban.

Sakataren hukumar, Dakta Anthony Ojukwu shi ne ya shaida hakan a makon jiya, yayin da ke gabatar da bayani kan yawan kesa-kesan cin zarafin mutane da aka samu a watan Mayu da ya gudana a Abuja. Ya nuna takaicinsa kan cewa kaso mafi tsoka na kauye hakkin an samesu ne kan masu madafin iko.

  • Me Yake Faruwa Da Kungiyar Brighton A Kakar Bana?
  • Haaland Ba Zai Samu Buga Wasan Man City Da Brighton Ba A Yau Alhamis

Ya kuma nuna damuwa kan cewa masu rike da madafun iko da ya dace a ce suke tabbatar da yin duk mai yiyuwa domin ganin an kare hakkin al’umma, ba wai su kasance ja gaba wajen tauye musu hakkinsu ba.

Ojukwu ya nuna cewa akwai bukatar gwamnatocin jihohi da na tarayya da su dauki kwararan matakan shawo kan cin zarafin mutane ta hanyar aiwatar da shirye-shiryen da za su inganta samar da ilimi ga kowa, kiwon lafiya, gidaje, da kuma samar da damarmakin ayyukan yi.

Ya ce hakan zai taimaka wajen kare hakkin jama’a da kuma ba su damar morar tattalin arzikinsu, jin dadi da walwa hadi da hakkin al’adu ba tare da nuna bam-bance-bambance ko tsangwama ba.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

Da yake nuna takaici kan yadda kashe-kashe da garkuwa da mutane ke ci gaba da karuwa, babban Lauyan Nijeriya (SAN) ya yi tambayar kan yadda ake samun karuwar kamewa da tsare ‘yan jarida a kasar nan, kari kan yawan kashe jami’an tsaro, karuwar cin zarafin yara kanana gami da tasirin sauye-sauyen tattalin arziki wanda a cewarsa hakan na kara rage wa jama’a jin dadin hakkinsu a fadin kasar nan.

Shugaban NHRC ya kuma nuna takaicin hukumar na cewa a watan Mayu, sun shaidi korafe-korafen keta wa yara kanana haddi tare da cewa sama da kesa-kesai 31,288 da 7,560 an shigar da su ne kan masu madafun iko da wadanda ba su rike da madafun iko a cikin wannan wa’adin.

Ya ce, wannan adadin na tauye hakkin jama’a na zuwa ne dukd a kokarin da hukumar ke yi na dakile hakan. Ya ce, dole ne a nanata muhimmanci da ke akwai wajen bin matakan da suka dace domin wanzar da gaskiya, da kuma tabbatar da cewa jami’an tsaro na bin matakan da suka dace daidai da yadda doka ya tanadar musu.

A cewarsa, hukumar ta kuma samu rahoton kashe-kashe 298 da garkuwa da mu-tane 360 a cikin watan na Mayu da ‘yan bindiga dadi suka aikata.

Ya bukaci gwamnati da ta tashi tsaye wajen magance matsalar tauye hakkin jama’a da kuma tabbatar da cewa jama’a na cin gajiyar tattalin arzikinsu, walwala da jin dadi da kuma al’adu ba tare da nuna bambanci ko tsangwama ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HukumaHuman rights
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Maraba Da Goyon Bayan Duk Wani Kokari Da Zai Taimaka Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya

Next Post

Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin Da Talata A Matsayin Ranakun Hutu

Related

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

3 hours ago
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi
Labarai

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

4 hours ago
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo
Labarai

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

4 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

5 hours ago
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 
Labarai

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

6 hours ago
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372
Labarai

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

7 hours ago
Next Post
Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin Da Talata A Matsayin Ranakun Hutu

Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin Da Talata A Matsayin Ranakun Hutu

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

August 12, 2025
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.