• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jami’an Saudiya Da Nijeriya Suka Yi Rangadin Wuraren Aikin Hajji

by Bello Hamza
1 year ago
in Addini, Labarai
0
Yadda Jami’an Saudiya Da Nijeriya Suka Yi Rangadin Wuraren Aikin Hajji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da aka kammala jigilar alhazan bana a ranar Lahadi 10 ga watan Yuni 2024 ba tare da wata matsalar a zo a gani ba, Hukumar Alhazan Nijeriya NAHCON ta ayyana ranar 22 ga watan Yuni na fara dawo da Alhazai gida bayan kammala aikin hajjin.

Domin tabbatar da an gudanar da aikin hajjin cikin nasara, Hukumar Alhaza NAHCON tare da Ma’aikatar Aikin Haji da Umara ta kasar Saudiya sun jagoranci shugabannin hukumar Alhazai na jihohi, ‘yan jarida da wakilan masu ruwa da tsaki zagayen gani da ido domin ganin irin shirin da hukumar ta yi a wurare masu tsarki da za su karbi bakuncin miliyoyin Alhazai daga sassan duniya, wuraren sun hada da Muna, Muzdalifa da kuma Arafat.

  • Hajjin Bana: Ofishin Jakadancin Saudiyya Ya Yi Bankwana Da Alhazan Nijeriya
  • Sabon Tsari: Alhazan Nijeriya Zasu Daina Daɗewa A Saudiyya

Jihohin da suka samu halartar wannan zagayen sun hada da Jihar Nasarawa, Oyo, Ogun, Kaduna, Kano, Yobe da kuma jihar Filato, sauran jihohin sun kuma hada da jihar Benuwai, Kebbi, Katsina, Sakkwato Zamfara da Jigawa. Haka kuma an samu hakartar ‘yan jarida daga kafafen watsa labarai da dama na gida Nijeriya da dana kasashen waje.

Shugaba mai kula da harkokin NAHCON a garin Makkah, Dakta Aliyu Tanko da Kwamishina mai kula da gudanarwa na NAHCON Prince Anofiu Olarenwaju Elegushi suka jagoranci zagayen, inda Dakta Aliyu Tanko ya bayyana irin shirin da hukumar kasar Saudiya ta yi a bangaren sake fasalin tantin da Alhazai za su zauna a ciki, inda aka sabunta na’urorin sanyaya dakuna (AC) a dukkan tantunan an kuma samar ban dakuna a kusa-kusa domin walwala da jin dadin Alhazai.

Wakilinmu ya kuma lura da yadda aka tanadi jami’an tsaro a dukkan bangarorin na Muna, Muzdalifa da kuma Arafat, “An samar da jami’an tsaron ne don tabbatar da komai ya tafi daidai a kuma samu nasarar dakile duk wata barazana da ka iya tasowa a yayin gudanar da wannan ibadar, ba ma son irin abin da ya faru a shekarun baya na turmutsitsi ya sake faruwa, inda ya yi sanadiyyar rasuwar Alhazai ‘yan Nijeriya 300,” in ji Dakta Aliyu Tanko.

Labarai Masu Nasaba

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

A kan haka, Dakta Aliyu Tanko ya nemi hadin kan dukkan masu ruwa da tsaki, musamman shugabannin alhazai na jihohi da ‘yan Jarida su karfafa gangamin fadakar da alhazai a kan bukatar bin doka da oda, su kuma bi umarni da dokokin da aka tsara a wadannan wuarre masu tsarki domin ganin an samar nasarar da ya kamata.

A nasa tsokacin, kwamishinan NAHCON mai kula da ayyuka Prince Anofiu Olarenwaju Elegushi, ya ce makasudin wannan ziyarar, ita ce domin hukumoimin Alhazai na jihohi sun fahimci irin tsarin da aka yi a wannan shekarar domin su san yadda za su ilimantar da alhazan su ta yadda za a kauce wa rudani a yayin gudanar da aikin hajji, “Zagayen wadannan wuraren ibada zai taimaka wa jami’an hukumar Alhazai sanin yadda za su tafiyar da alhazansu a wurare masu tsarki na Muna, Arafat da kuma Muzdalifa.

Ya kuma nemi Alhazai su kare kansu daga tsananin zafin da za a fuskanta a ‘yan kwanakin nan a kasar Saudiya, saboda haka su guji yawo a cikin rana ba tare da wani dalili ba, “Dokokin addnin Musulunci ba su ce dole sai mutum ya hau kan dutsen Arafat (Jabalur-Rahma) ba a yayin tsayiwar Arfat, wannan ma ya zama dole saboda irin cutar da za a iya fuskanta a wannan lokacin,’’ in ji shi.

A wani bangaren kuma Hukumnar Alhazai ta NAHCON ta sanar da samun nasarar jigilar Alhazan bana daga jihohi 15, sun kuma hada da Kaduna, Bauchi, Bayelsa, Benuwai, Delta, Ebonyi, Edo, Ekiti, Enugu, Imo, Kogi, Oyo, Osun, Taraba, Ribas da kuma alhazai na bangaren runudunoni tsaro.

Sauran jihohin da aka kammala jigilar Alhazan jihohisu sun hada da Kebbi, Adamawa, Borno, Gombe, Jigawa, Kwara, Ogun, Yobe da yankin Babban Birni Tarayya Abuja, inda Alhazan wadannan jihohin da dama suka gama zaman su na garin Madina kuma sun isa garin Makka domin gudanar da ainihin aikin hajjin bana.

Idan ba a manta ba kamfanonin jirage uku ne suka yi jiglar Maniyyatan Nijeriya zuwa kasa mai tsarki a wannan shekarar sun kuma hada da Flynas, Mad Air da kuma Air Peace.

Ya zuwa ranar Asabar din nan kamfanin jigilar Alhazai na Flynas ya yi sawu 45 da adadin Maniyata 18,727 abin da ya bashi kashi 94% cikin dari na jigilar Maniyatan da zai kwasa daga gida Nijeriya zuwa kasa mai tsarki.

Kamfanin Mad Air ya yi sawu 48 inda ya dauki adadin Maniyata 23,233 abinda ya bashi kashi 97% cikin dari na Maniyatan da yake jigila.

Haka kuma kamfanin jiragen sama na Air Peace ya yi sawu 24 ya yi jigilar Alhazai 7, 293.

Bayanin da ya fito daga shasin tattara bayanai na NAHCON, kamfanonin jiragen saman gaba dayan su sun yi sawu 117 nda a ciki suka kwashi alhazai fiye da 49,253.

Daga cikin wannan adadin Maniyyata 7,566 ne kadai suka sauka a filin jirgin sama na Sarki Abdulaziz da ke Jidda, jirage 101 duk sun sauka ne a filin saukar jirage na Yarima Muhammad bin Abdulaziz da ke Birnin Madinah.

A yawan Maniyyata 49,253 da muke da su a Kasar ta Saudiya, Maniyyata maza muna da mutum 30,658 yayin da muke da maniyyata mata 18,595.

Daga cikin adadin jimlar, Maniyata 10,525 ne suke birnin Madina, inda Maniyata 38,728 suka kammala aikin Umura, suna zaune a garin Makkah suna jiran lokacin fita Muna domin gudanar da aikin Hajji na wannan shekara 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HajjSaudiSaudiyyaUmarah
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: A Bara Darajar Cinikayya Tsakanin Kasashen Shiyya Karkashin RCEP Ta Kai Dala Triliyan 5.6

Next Post

Sin Na Da Hakkin Shigar Da Kara Gaban WTO Kan Sabbin Harajin EU Kan EVs Na Sin

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

53 seconds ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

2 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

14 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

16 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

18 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

21 hours ago
Next Post
Sin Na Da Hakkin Shigar Da Kara Gaban WTO Kan Sabbin Harajin EU Kan EVs Na Sin

Sin Na Da Hakkin Shigar Da Kara Gaban WTO Kan Sabbin Harajin EU Kan EVs Na Sin

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.