ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jami’an Saudiya Da Nijeriya Suka Yi Rangadin Wuraren Aikin Hajji

by Bello Hamza
2 years ago
Nijeriya

A yayin da aka kammala jigilar alhazan bana a ranar Lahadi 10 ga watan Yuni 2024 ba tare da wata matsalar a zo a gani ba, Hukumar Alhazan Nijeriya NAHCON ta ayyana ranar 22 ga watan Yuni na fara dawo da Alhazai gida bayan kammala aikin hajjin.

Domin tabbatar da an gudanar da aikin hajjin cikin nasara, Hukumar Alhaza NAHCON tare da Ma’aikatar Aikin Haji da Umara ta kasar Saudiya sun jagoranci shugabannin hukumar Alhazai na jihohi, ‘yan jarida da wakilan masu ruwa da tsaki zagayen gani da ido domin ganin irin shirin da hukumar ta yi a wurare masu tsarki da za su karbi bakuncin miliyoyin Alhazai daga sassan duniya, wuraren sun hada da Muna, Muzdalifa da kuma Arafat.

  • Hajjin Bana: Ofishin Jakadancin Saudiyya Ya Yi Bankwana Da Alhazan Nijeriya
  • Sabon Tsari: Alhazan Nijeriya Zasu Daina Daɗewa A Saudiyya

Jihohin da suka samu halartar wannan zagayen sun hada da Jihar Nasarawa, Oyo, Ogun, Kaduna, Kano, Yobe da kuma jihar Filato, sauran jihohin sun kuma hada da jihar Benuwai, Kebbi, Katsina, Sakkwato Zamfara da Jigawa. Haka kuma an samu hakartar ‘yan jarida daga kafafen watsa labarai da dama na gida Nijeriya da dana kasashen waje.

ADVERTISEMENT

Shugaba mai kula da harkokin NAHCON a garin Makkah, Dakta Aliyu Tanko da Kwamishina mai kula da gudanarwa na NAHCON Prince Anofiu Olarenwaju Elegushi suka jagoranci zagayen, inda Dakta Aliyu Tanko ya bayyana irin shirin da hukumar kasar Saudiya ta yi a bangaren sake fasalin tantin da Alhazai za su zauna a ciki, inda aka sabunta na’urorin sanyaya dakuna (AC) a dukkan tantunan an kuma samar ban dakuna a kusa-kusa domin walwala da jin dadin Alhazai.

Wakilinmu ya kuma lura da yadda aka tanadi jami’an tsaro a dukkan bangarorin na Muna, Muzdalifa da kuma Arafat, “An samar da jami’an tsaron ne don tabbatar da komai ya tafi daidai a kuma samu nasarar dakile duk wata barazana da ka iya tasowa a yayin gudanar da wannan ibadar, ba ma son irin abin da ya faru a shekarun baya na turmutsitsi ya sake faruwa, inda ya yi sanadiyyar rasuwar Alhazai ‘yan Nijeriya 300,” in ji Dakta Aliyu Tanko.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

A kan haka, Dakta Aliyu Tanko ya nemi hadin kan dukkan masu ruwa da tsaki, musamman shugabannin alhazai na jihohi da ‘yan Jarida su karfafa gangamin fadakar da alhazai a kan bukatar bin doka da oda, su kuma bi umarni da dokokin da aka tsara a wadannan wuarre masu tsarki domin ganin an samar nasarar da ya kamata.

A nasa tsokacin, kwamishinan NAHCON mai kula da ayyuka Prince Anofiu Olarenwaju Elegushi, ya ce makasudin wannan ziyarar, ita ce domin hukumoimin Alhazai na jihohi sun fahimci irin tsarin da aka yi a wannan shekarar domin su san yadda za su ilimantar da alhazan su ta yadda za a kauce wa rudani a yayin gudanar da aikin hajji, “Zagayen wadannan wuraren ibada zai taimaka wa jami’an hukumar Alhazai sanin yadda za su tafiyar da alhazansu a wurare masu tsarki na Muna, Arafat da kuma Muzdalifa.

Ya kuma nemi Alhazai su kare kansu daga tsananin zafin da za a fuskanta a ‘yan kwanakin nan a kasar Saudiya, saboda haka su guji yawo a cikin rana ba tare da wani dalili ba, “Dokokin addnin Musulunci ba su ce dole sai mutum ya hau kan dutsen Arafat (Jabalur-Rahma) ba a yayin tsayiwar Arfat, wannan ma ya zama dole saboda irin cutar da za a iya fuskanta a wannan lokacin,’’ in ji shi.

A wani bangaren kuma Hukumnar Alhazai ta NAHCON ta sanar da samun nasarar jigilar Alhazan bana daga jihohi 15, sun kuma hada da Kaduna, Bauchi, Bayelsa, Benuwai, Delta, Ebonyi, Edo, Ekiti, Enugu, Imo, Kogi, Oyo, Osun, Taraba, Ribas da kuma alhazai na bangaren runudunoni tsaro.

Sauran jihohin da aka kammala jigilar Alhazan jihohisu sun hada da Kebbi, Adamawa, Borno, Gombe, Jigawa, Kwara, Ogun, Yobe da yankin Babban Birni Tarayya Abuja, inda Alhazan wadannan jihohin da dama suka gama zaman su na garin Madina kuma sun isa garin Makka domin gudanar da ainihin aikin hajjin bana.

Idan ba a manta ba kamfanonin jirage uku ne suka yi jiglar Maniyyatan Nijeriya zuwa kasa mai tsarki a wannan shekarar sun kuma hada da Flynas, Mad Air da kuma Air Peace.

Ya zuwa ranar Asabar din nan kamfanin jigilar Alhazai na Flynas ya yi sawu 45 da adadin Maniyata 18,727 abin da ya bashi kashi 94% cikin dari na jigilar Maniyatan da zai kwasa daga gida Nijeriya zuwa kasa mai tsarki.

Kamfanin Mad Air ya yi sawu 48 inda ya dauki adadin Maniyata 23,233 abinda ya bashi kashi 97% cikin dari na Maniyatan da yake jigila.

Haka kuma kamfanin jiragen sama na Air Peace ya yi sawu 24 ya yi jigilar Alhazai 7, 293.

Bayanin da ya fito daga shasin tattara bayanai na NAHCON, kamfanonin jiragen saman gaba dayan su sun yi sawu 117 nda a ciki suka kwashi alhazai fiye da 49,253.

Daga cikin wannan adadin Maniyyata 7,566 ne kadai suka sauka a filin jirgin sama na Sarki Abdulaziz da ke Jidda, jirage 101 duk sun sauka ne a filin saukar jirage na Yarima Muhammad bin Abdulaziz da ke Birnin Madinah.

A yawan Maniyyata 49,253 da muke da su a Kasar ta Saudiya, Maniyyata maza muna da mutum 30,658 yayin da muke da maniyyata mata 18,595.

Daga cikin adadin jimlar, Maniyata 10,525 ne suke birnin Madina, inda Maniyata 38,728 suka kammala aikin Umura, suna zaune a garin Makkah suna jiran lokacin fita Muna domin gudanar da aikin Hajji na wannan shekara 2024.

Nijeriya
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Sin Na Da Hakkin Shigar Da Kara Gaban WTO Kan Sabbin Harajin EU Kan EVs Na Sin

Sin Na Da Hakkin Shigar Da Kara Gaban WTO Kan Sabbin Harajin EU Kan EVs Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.