ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jami’an Saudiya Da Nijeriya Suka Yi Rangadin Wuraren Aikin Hajji

by Bello Hamza
2 years ago
Nijeriya

A yayin da aka kammala jigilar alhazan bana a ranar Lahadi 10 ga watan Yuni 2024 ba tare da wata matsalar a zo a gani ba, Hukumar Alhazan Nijeriya NAHCON ta ayyana ranar 22 ga watan Yuni na fara dawo da Alhazai gida bayan kammala aikin hajjin.

Domin tabbatar da an gudanar da aikin hajjin cikin nasara, Hukumar Alhaza NAHCON tare da Ma’aikatar Aikin Haji da Umara ta kasar Saudiya sun jagoranci shugabannin hukumar Alhazai na jihohi, ‘yan jarida da wakilan masu ruwa da tsaki zagayen gani da ido domin ganin irin shirin da hukumar ta yi a wurare masu tsarki da za su karbi bakuncin miliyoyin Alhazai daga sassan duniya, wuraren sun hada da Muna, Muzdalifa da kuma Arafat.

  • Hajjin Bana: Ofishin Jakadancin Saudiyya Ya Yi Bankwana Da Alhazan Nijeriya
  • Sabon Tsari: Alhazan Nijeriya Zasu Daina Daɗewa A Saudiyya

Jihohin da suka samu halartar wannan zagayen sun hada da Jihar Nasarawa, Oyo, Ogun, Kaduna, Kano, Yobe da kuma jihar Filato, sauran jihohin sun kuma hada da jihar Benuwai, Kebbi, Katsina, Sakkwato Zamfara da Jigawa. Haka kuma an samu hakartar ‘yan jarida daga kafafen watsa labarai da dama na gida Nijeriya da dana kasashen waje.

ADVERTISEMENT

Shugaba mai kula da harkokin NAHCON a garin Makkah, Dakta Aliyu Tanko da Kwamishina mai kula da gudanarwa na NAHCON Prince Anofiu Olarenwaju Elegushi suka jagoranci zagayen, inda Dakta Aliyu Tanko ya bayyana irin shirin da hukumar kasar Saudiya ta yi a bangaren sake fasalin tantin da Alhazai za su zauna a ciki, inda aka sabunta na’urorin sanyaya dakuna (AC) a dukkan tantunan an kuma samar ban dakuna a kusa-kusa domin walwala da jin dadin Alhazai.

Wakilinmu ya kuma lura da yadda aka tanadi jami’an tsaro a dukkan bangarorin na Muna, Muzdalifa da kuma Arafat, “An samar da jami’an tsaron ne don tabbatar da komai ya tafi daidai a kuma samu nasarar dakile duk wata barazana da ka iya tasowa a yayin gudanar da wannan ibadar, ba ma son irin abin da ya faru a shekarun baya na turmutsitsi ya sake faruwa, inda ya yi sanadiyyar rasuwar Alhazai ‘yan Nijeriya 300,” in ji Dakta Aliyu Tanko.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

A kan haka, Dakta Aliyu Tanko ya nemi hadin kan dukkan masu ruwa da tsaki, musamman shugabannin alhazai na jihohi da ‘yan Jarida su karfafa gangamin fadakar da alhazai a kan bukatar bin doka da oda, su kuma bi umarni da dokokin da aka tsara a wadannan wuarre masu tsarki domin ganin an samar nasarar da ya kamata.

A nasa tsokacin, kwamishinan NAHCON mai kula da ayyuka Prince Anofiu Olarenwaju Elegushi, ya ce makasudin wannan ziyarar, ita ce domin hukumoimin Alhazai na jihohi sun fahimci irin tsarin da aka yi a wannan shekarar domin su san yadda za su ilimantar da alhazan su ta yadda za a kauce wa rudani a yayin gudanar da aikin hajji, “Zagayen wadannan wuraren ibada zai taimaka wa jami’an hukumar Alhazai sanin yadda za su tafiyar da alhazansu a wurare masu tsarki na Muna, Arafat da kuma Muzdalifa.

Ya kuma nemi Alhazai su kare kansu daga tsananin zafin da za a fuskanta a ‘yan kwanakin nan a kasar Saudiya, saboda haka su guji yawo a cikin rana ba tare da wani dalili ba, “Dokokin addnin Musulunci ba su ce dole sai mutum ya hau kan dutsen Arafat (Jabalur-Rahma) ba a yayin tsayiwar Arfat, wannan ma ya zama dole saboda irin cutar da za a iya fuskanta a wannan lokacin,’’ in ji shi.

A wani bangaren kuma Hukumnar Alhazai ta NAHCON ta sanar da samun nasarar jigilar Alhazan bana daga jihohi 15, sun kuma hada da Kaduna, Bauchi, Bayelsa, Benuwai, Delta, Ebonyi, Edo, Ekiti, Enugu, Imo, Kogi, Oyo, Osun, Taraba, Ribas da kuma alhazai na bangaren runudunoni tsaro.

Sauran jihohin da aka kammala jigilar Alhazan jihohisu sun hada da Kebbi, Adamawa, Borno, Gombe, Jigawa, Kwara, Ogun, Yobe da yankin Babban Birni Tarayya Abuja, inda Alhazan wadannan jihohin da dama suka gama zaman su na garin Madina kuma sun isa garin Makka domin gudanar da ainihin aikin hajjin bana.

Idan ba a manta ba kamfanonin jirage uku ne suka yi jiglar Maniyyatan Nijeriya zuwa kasa mai tsarki a wannan shekarar sun kuma hada da Flynas, Mad Air da kuma Air Peace.

Ya zuwa ranar Asabar din nan kamfanin jigilar Alhazai na Flynas ya yi sawu 45 da adadin Maniyata 18,727 abin da ya bashi kashi 94% cikin dari na jigilar Maniyatan da zai kwasa daga gida Nijeriya zuwa kasa mai tsarki.

Kamfanin Mad Air ya yi sawu 48 inda ya dauki adadin Maniyata 23,233 abinda ya bashi kashi 97% cikin dari na Maniyatan da yake jigila.

Haka kuma kamfanin jiragen sama na Air Peace ya yi sawu 24 ya yi jigilar Alhazai 7, 293.

Bayanin da ya fito daga shasin tattara bayanai na NAHCON, kamfanonin jiragen saman gaba dayan su sun yi sawu 117 nda a ciki suka kwashi alhazai fiye da 49,253.

Daga cikin wannan adadin Maniyyata 7,566 ne kadai suka sauka a filin jirgin sama na Sarki Abdulaziz da ke Jidda, jirage 101 duk sun sauka ne a filin saukar jirage na Yarima Muhammad bin Abdulaziz da ke Birnin Madinah.

A yawan Maniyyata 49,253 da muke da su a Kasar ta Saudiya, Maniyyata maza muna da mutum 30,658 yayin da muke da maniyyata mata 18,595.

Daga cikin adadin jimlar, Maniyata 10,525 ne suke birnin Madina, inda Maniyata 38,728 suka kammala aikin Umura, suna zaune a garin Makkah suna jiran lokacin fita Muna domin gudanar da aikin Hajji na wannan shekara 2024.

Nijeriya
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Sin Na Da Hakkin Shigar Da Kara Gaban WTO Kan Sabbin Harajin EU Kan EVs Na Sin

Sin Na Da Hakkin Shigar Da Kara Gaban WTO Kan Sabbin Harajin EU Kan EVs Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.