• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Shekara 13 Ya Kashe Kansa Bayan Jami’an Tsaro Sun Azabtar Da shi

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Tsaro
0
Ɗan Shekara 13 Ya Kashe Kansa Bayan Jami’an Tsaro Sun Azabtar Da shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani yaro mai shekaru 13 mai suna Wisdom Hashimu ya mutu ta hanyar rataye kansa a Unguwar Maigero da ke Karamar Hukumar Chikun a Jihar Kaduna.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne bayan wani soja da jami’an rundunar hadin gwiwa ta Cibilian Task Force a yankin sun azabtar da marigayin.

  • Sojoji Sun Kashe Boko Haram 4 A Borno
  • Boko Haram Sun Sace Fasinjoji A Kan Hanyar Maiduguri Zuwa Kano

Marigayi Wisdom wadda ta aikata wannan aika-aika a harabar gidan da ke kan titin Lafiya Sarki an ce an zarge shi da laifin satar Naira 10,000 daga wata makwabciyarsu a ranar.

A wani rahoto da gidan Talabijin na Channels TB ta fitar, makwabciyarta mai shekaru 16 mai suna Hope, an ce ta gayyaci saurayinta mai suna Segun Samson, wanda soja ne a sansanin Bodi da ke Fatakwal, babban birnin jihar Ribers wanda ya shiga cikin maganar.

Sai dai an nemi kudi an rasa a lokacin ziyarar, wanda hakan ya sa Hope ta hada saurayin nata da Wisdom da kuma dan uwanta zuwa ofishin Cibilian JTF.

Labarai Masu Nasaba

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

Wisdom wacce ke zana jarabawar Karamar Sakandare, an bayyana cewa wani soja da jami’an Cibilian JTF ne suka yi masa mugun duka.

Mahaifin Wisdom, Mista Saul, wanda ya zanta da manema labarai ya ce, “Maimakon su kai rahoto ga ‘yansanda, sai kawai sojan ya ja dan’uwan Wisdom da Hope, wadanda ake zargi da satar kudin zuwa ofishin cibilian JTF.

“A ofishin cibilian JTF, an yi wa Wisdom mugun duka har ya kasa tafiya. Ya koma gida inda aka fara kula da lafiyarsa.”

Sai dai kuma wani abin takaici da ya afku shi ne an tsinci gawar Wisdom ya rataye kansa a bayan gidansu.

Sai dai a yayin da yake magana cikin bacin rai, mahaifin ya ce ‘yan Cibilian JTF sun dauki doka a hannunsu ta hanyar azabtar da Wisdom.

“Amma, ni abin da tunanina ya bani, Cibilian JTF ne kawai suka lakada wa Wisdom duka har ta kai ga suma, yayin da kanin Hope ya tsira ya dawo gida.

“Bayan an yi mata tambayoyi a gida, kaninta Hope ya amsa laifin da ya aikata, bayan da aka gano Naira 9,000 a aljihunsa, ya ce ya riga ya kashe Naira 1,000,” a cewarsa.

Don haka dangin sun bukaci a yi adalci kan azabtarwa da ake zargin marigayi dansu wanda hakan ya kai ga kashe shi.

“Tun daga lokacin aka fara bincike. Kwamishinan ‘yansandan ya umarci sashen binciken manyan laifuka da ya dauki nauyin lamarin kuma duk wanda ke da hannu za a gurfanar da shi a gaban kotu domin tabbatar da adalci”

Wisdom da ke zana jarabawar karamar Sakandare, an bayyana cewa wani soja da jami’an Cibilian JTF ne suka yi masa mugun duka.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, Mansir Hassan, ya ce an fara bincike kan lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramBornoCJTFMaiduguriTsaroZulum
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping: Ba Zan Ci Amanar Jama’a Ba

Next Post

Xi Jinping: Sa Mutane A Matsayi Mafi Muhimmanci A Zuciya

Related

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ
Tsaro

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

1 week ago
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi
Labarai

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

1 week ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

2 weeks ago
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

2 weeks ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku

3 weeks ago
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja
Tsaro

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

4 weeks ago
Next Post
Xi Jinping: Sa Mutane A Matsayi Mafi Muhimmanci A Zuciya

Xi Jinping: Sa Mutane A Matsayi Mafi Muhimmanci A Zuciya

LABARAI MASU NASABA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.