• English
  • Business News
Thursday, September 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojin Nijeriya Ta Musanta Zargin Cin Zarafin Matan Da Suka Tsira Daga Boko Haram

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Tsaro
0
Sojin Nijeriya Ta Musanta Zargin Cin Zarafin Matan Da Suka Tsira Daga Boko Haram
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar Sojin Nijeriyta ta musanta zargin cin zarafin matan da suka tsira daga hannun boko haram a yankin arewa maso gabas.

Daraktan yada labarai na shalkwatar tsaron Nijeriya, Manjo Janar Edward Buba wanda ya mayar da martini game da zargin da Kungiyar Kare Hakkin Dan’adam ta Amnesty ta yi, ya ce dakarun Nijeriya suna aiki ne bisa kwarewa daidai da yadda doka ta tsara kuma ba tare da take hakkin bil’adama ba.

  • Mayaƙan ISWAP Da Boko Haram 4 Sun Tuba Sun Miƙa Wuya A Borno
  • Gwamnatin Kano Ta Bude Makarantun Da Ganduje Ya Rufe

Ya yi kira ga kungiyoyin kare hakkin Dan’adam su rika tuntubar rundunarsu da zarar sun ji wani abu domin tantance gaskiya kafin su kai ga yada wa duniya, domin hakan shi ne adalci.

A wani sabon rahoto da ta fitar, Kungiyar Kare Hakkin Bil’adama ta Amnesty International ta bayyana cewa an tsare mata da ‘yan mata ba bisa ka’ida ba an kuma ci zarafinsu a cibiyoyin tsare mutane na sojojin Nijeriya bayan da suka tsere daga hannun mayakan Boko Haram.

Rahoton ya ce an tsare wasu daga cikin matan tare da ‘ya’yansu tsawon shekaru saboda kawai zargin suna da alaka da kungiyar masu tsattsauran ra’ayin. Kungiyar Amnesty ta ambaci hirarraki 126, galibi da wadanda suka tsira daga wannan mummunan yanayin, a cikin shekaru 14 da masu tsattsauran ra’ayin addinin Islaman suka kwashe suna kaddamar da hare-hare.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

Rahoton ya sake bayyana damauwa akan keta hakkokin bil’adama da aka zargi sojojin Nijeriya da yi, wadanda a baya aka zarge su da aikata hukuncin kisa na wuce gona da iri da kuma yin kame ba bisa ka’ida ba, a daya daga cikin rikice-rikice mafi dadewa da aka gani a duniya.

Ko da yake, rahoton ya lura cewa dabi’ar tsare mutane ba bisa ka’ida ba na tsawon lokaci bai bazu ba a cikin ‘yan shekarun nan.

Rundunar sojan Nijeriya ta yi watsi da rahoton a matsayin “mara tushe” kuma ta nanata cewa ta samu ci gaba wajen inganta kare hakkokin bil’adama kuma tana hukunta jami’anta da suka yi ba daidai ba.

Amma yanayin da wasu matan suka tsinci kansu a ciki bayan da suka tsere daga hannun ‘yan Boko Haram na da matukar muni, lamarin da ya sa wasunsu suka gwammace su koma wa ‘yan Boko Haram, abin da Niki Frederiek, mai bincike kan rikice-rikice na kungiyar Amnesty International, ya fada kenan game da cibiyoyin da ake tsare mutane a sansanonin soja da ke Jihar Borno.

Rahoton ya ce akalla mutum 31 da suka tsira da aka yi hira da su sun ce an tsare su ba bisa ka’ida ba a cibiyoyin, abin da ke nuna cewa wannan dabi’ar ta bazu.

“Dole ne hukumomin Nijeriya su tallafa wa wadannan ‘yan mata da mata yayin da suka koma cikin al’umma,” in ji Samira Daoud, Daraktar Kungiyar Amnesty International a Yammaci da Tsakiyar Afirka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArmyHuman rightsSojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sadaukar Da Kai Ga Hidimtawa Jama’a: Tasirin Mahaifin Xi Jinping A Kan Dansa

Next Post

Jirgin Kasa Mai Saurin Tafiya Da Ya Hada Babban Yankin Sin Da Hong kong Ya Fara Aiki

Related

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

3 days ago
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku
Tsaro

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

4 days ago
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

5 days ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Ceto Wani Dan Shekara 25 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

2 weeks ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Tsaro

An Cafke Mutum Hudu Bayan ‘Yan Fashi 20 Sun Afka Wasu Gidaje A Bauchi

2 weeks ago
NDLEA Ta Kama Wani Matashi Dan Shekara 29 Da Kwayoyin Tramadol 7,000 A Kano
Tsaro

NDLEA Ta Kama Wani Matashi Dan Shekara 29 Da Kwayoyin Tramadol 7,000 A Kano

2 weeks ago
Next Post
Jirgin Kasa Mai Saurin Tafiya Da Ya Hada Babban Yankin Sin Da Hong kong Ya Fara Aiki

Jirgin Kasa Mai Saurin Tafiya Da Ya Hada Babban Yankin Sin Da Hong kong Ya Fara Aiki

LABARAI MASU NASABA

Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

September 11, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

September 11, 2025
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

September 11, 2025
Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

September 10, 2025
Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

September 10, 2025
Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

September 10, 2025
Akwai Bukatar Tinubu Ya Rubanya Kokarin Buhari Na Bunkasa Harkokin Noma  -Alhaji Umar

Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi 1 Ga Oktoba

September 10, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025

September 10, 2025
“Hadin Kan Kasashen BRICS” Ya Karfafa Shawo Kan Kalubale

“Hadin Kan Kasashen BRICS” Ya Karfafa Shawo Kan Kalubale

September 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.