ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojin Nijeriya Ta Musanta Zargin Cin Zarafin Matan Da Suka Tsira Daga Boko Haram

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Nijeriya

Rundunar Sojin Nijeriyta ta musanta zargin cin zarafin matan da suka tsira daga hannun boko haram a yankin arewa maso gabas.

Daraktan yada labarai na shalkwatar tsaron Nijeriya, Manjo Janar Edward Buba wanda ya mayar da martini game da zargin da Kungiyar Kare Hakkin Dan’adam ta Amnesty ta yi, ya ce dakarun Nijeriya suna aiki ne bisa kwarewa daidai da yadda doka ta tsara kuma ba tare da take hakkin bil’adama ba.

  • Mayaƙan ISWAP Da Boko Haram 4 Sun Tuba Sun Miƙa Wuya A Borno
  • Gwamnatin Kano Ta Bude Makarantun Da Ganduje Ya Rufe

Ya yi kira ga kungiyoyin kare hakkin Dan’adam su rika tuntubar rundunarsu da zarar sun ji wani abu domin tantance gaskiya kafin su kai ga yada wa duniya, domin hakan shi ne adalci.

ADVERTISEMENT

A wani sabon rahoto da ta fitar, Kungiyar Kare Hakkin Bil’adama ta Amnesty International ta bayyana cewa an tsare mata da ‘yan mata ba bisa ka’ida ba an kuma ci zarafinsu a cibiyoyin tsare mutane na sojojin Nijeriya bayan da suka tsere daga hannun mayakan Boko Haram.

Rahoton ya ce an tsare wasu daga cikin matan tare da ‘ya’yansu tsawon shekaru saboda kawai zargin suna da alaka da kungiyar masu tsattsauran ra’ayin. Kungiyar Amnesty ta ambaci hirarraki 126, galibi da wadanda suka tsira daga wannan mummunan yanayin, a cikin shekaru 14 da masu tsattsauran ra’ayin addinin Islaman suka kwashe suna kaddamar da hare-hare.

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Rahoton ya sake bayyana damauwa akan keta hakkokin bil’adama da aka zargi sojojin Nijeriya da yi, wadanda a baya aka zarge su da aikata hukuncin kisa na wuce gona da iri da kuma yin kame ba bisa ka’ida ba, a daya daga cikin rikice-rikice mafi dadewa da aka gani a duniya.

Ko da yake, rahoton ya lura cewa dabi’ar tsare mutane ba bisa ka’ida ba na tsawon lokaci bai bazu ba a cikin ‘yan shekarun nan.

Rundunar sojan Nijeriya ta yi watsi da rahoton a matsayin “mara tushe” kuma ta nanata cewa ta samu ci gaba wajen inganta kare hakkokin bil’adama kuma tana hukunta jami’anta da suka yi ba daidai ba.

Amma yanayin da wasu matan suka tsinci kansu a ciki bayan da suka tsere daga hannun ‘yan Boko Haram na da matukar muni, lamarin da ya sa wasunsu suka gwammace su koma wa ‘yan Boko Haram, abin da Niki Frederiek, mai bincike kan rikice-rikice na kungiyar Amnesty International, ya fada kenan game da cibiyoyin da ake tsare mutane a sansanonin soja da ke Jihar Borno.

Rahoton ya ce akalla mutum 31 da suka tsira da aka yi hira da su sun ce an tsare su ba bisa ka’ida ba a cibiyoyin, abin da ke nuna cewa wannan dabi’ar ta bazu.

“Dole ne hukumomin Nijeriya su tallafa wa wadannan ‘yan mata da mata yayin da suka koma cikin al’umma,” in ji Samira Daoud, Daraktar Kungiyar Amnesty International a Yammaci da Tsakiyar Afirka.

Nijeriya
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Next Post
Jirgin Kasa Mai Saurin Tafiya Da Ya Hada Babban Yankin Sin Da Hong kong Ya Fara Aiki

Jirgin Kasa Mai Saurin Tafiya Da Ya Hada Babban Yankin Sin Da Hong kong Ya Fara Aiki

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.