ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojin Nijeriya Ta Musanta Zargin Cin Zarafin Matan Da Suka Tsira Daga Boko Haram

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Nijeriya

Rundunar Sojin Nijeriyta ta musanta zargin cin zarafin matan da suka tsira daga hannun boko haram a yankin arewa maso gabas.

Daraktan yada labarai na shalkwatar tsaron Nijeriya, Manjo Janar Edward Buba wanda ya mayar da martini game da zargin da Kungiyar Kare Hakkin Dan’adam ta Amnesty ta yi, ya ce dakarun Nijeriya suna aiki ne bisa kwarewa daidai da yadda doka ta tsara kuma ba tare da take hakkin bil’adama ba.

  • Mayaƙan ISWAP Da Boko Haram 4 Sun Tuba Sun Miƙa Wuya A Borno
  • Gwamnatin Kano Ta Bude Makarantun Da Ganduje Ya Rufe

Ya yi kira ga kungiyoyin kare hakkin Dan’adam su rika tuntubar rundunarsu da zarar sun ji wani abu domin tantance gaskiya kafin su kai ga yada wa duniya, domin hakan shi ne adalci.

ADVERTISEMENT

A wani sabon rahoto da ta fitar, Kungiyar Kare Hakkin Bil’adama ta Amnesty International ta bayyana cewa an tsare mata da ‘yan mata ba bisa ka’ida ba an kuma ci zarafinsu a cibiyoyin tsare mutane na sojojin Nijeriya bayan da suka tsere daga hannun mayakan Boko Haram.

Rahoton ya ce an tsare wasu daga cikin matan tare da ‘ya’yansu tsawon shekaru saboda kawai zargin suna da alaka da kungiyar masu tsattsauran ra’ayin. Kungiyar Amnesty ta ambaci hirarraki 126, galibi da wadanda suka tsira daga wannan mummunan yanayin, a cikin shekaru 14 da masu tsattsauran ra’ayin addinin Islaman suka kwashe suna kaddamar da hare-hare.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

Rahoton ya sake bayyana damauwa akan keta hakkokin bil’adama da aka zargi sojojin Nijeriya da yi, wadanda a baya aka zarge su da aikata hukuncin kisa na wuce gona da iri da kuma yin kame ba bisa ka’ida ba, a daya daga cikin rikice-rikice mafi dadewa da aka gani a duniya.

Ko da yake, rahoton ya lura cewa dabi’ar tsare mutane ba bisa ka’ida ba na tsawon lokaci bai bazu ba a cikin ‘yan shekarun nan.

Rundunar sojan Nijeriya ta yi watsi da rahoton a matsayin “mara tushe” kuma ta nanata cewa ta samu ci gaba wajen inganta kare hakkokin bil’adama kuma tana hukunta jami’anta da suka yi ba daidai ba.

Amma yanayin da wasu matan suka tsinci kansu a ciki bayan da suka tsere daga hannun ‘yan Boko Haram na da matukar muni, lamarin da ya sa wasunsu suka gwammace su koma wa ‘yan Boko Haram, abin da Niki Frederiek, mai bincike kan rikice-rikice na kungiyar Amnesty International, ya fada kenan game da cibiyoyin da ake tsare mutane a sansanonin soja da ke Jihar Borno.

Rahoton ya ce akalla mutum 31 da suka tsira da aka yi hira da su sun ce an tsare su ba bisa ka’ida ba a cibiyoyin, abin da ke nuna cewa wannan dabi’ar ta bazu.

“Dole ne hukumomin Nijeriya su tallafa wa wadannan ‘yan mata da mata yayin da suka koma cikin al’umma,” in ji Samira Daoud, Daraktar Kungiyar Amnesty International a Yammaci da Tsakiyar Afirka.

Nijeriya
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

June 1, 2026
NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
Tsaro

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

May 31, 2026
Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP
Tsaro

Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP

May 31, 2026
Next Post
Jirgin Kasa Mai Saurin Tafiya Da Ya Hada Babban Yankin Sin Da Hong kong Ya Fara Aiki

Jirgin Kasa Mai Saurin Tafiya Da Ya Hada Babban Yankin Sin Da Hong kong Ya Fara Aiki

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.