• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Kogi Ta Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Noma Da Kungiyar Solidaridad

by Abubakar Abba
1 year ago
Kogi

Gwamnatin Jihar Kogi ta kulla yarjeniya da kungiyar aikin noma ta kasa da kasa (Solidaridad), don kara bunkasa fannin aikin noma da kuma kara samar da wadataccen abinci a jihar da ma kasa baki-daya.

Gwamnan Jihar, Ahmed Usman Ododo ne ya bayyana haka a lokacin kaddamar da aikin noma kashi na biyu da aka gudanar a babban birnin tarrayya Abuja.

  • Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin
  • Shettima Ya Ƙaddamar Da Ginin Ofishin Hukumar Raya Arewa Maso Gabas

Ododo ya bayyana hakan ne ta bakin Sakatariyar Gwamnatin Jihar, Dakta Folashade Arike Ayoade.

Har ila yau, ya bayyana cewa; gwamnatin tasa ta sha alwashin inganta

aikin noma a jihar, musamman duba da ganin yadda ta mallaki babbar gonar da ke garin Suleja a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

A cewar tata, Allah ya albarkaci jihar da dimbin damammaki a wannan bangare na aikin noma tare kuma da ingantacciyar kasar noman.

Har ila yau kuma, ta yaba wa kungiyar ta Solidaridad da kuma NIPCONS, bisa tunawa da jihar ta Kogi a bangaren aikin noma da suka yi.

Folashade ta kuma bayar da tabbacin mayar da hankalin gwamnatin jihar, wajen kara habaka fannin aikin noma a fadin jihar baki-daya.

Haka zalika, ta yaba wa Gwamnatocin Kasar Amurka da Netherlands; kan yin hadaka a kan shirin na habaka aikin noma na jihar.

Ta kara da cewa, babu shakka al’ummar jihar da dama sun amfana da ayyukan wannan kungiya ta NISCOPS.

Ta ci gaba da cewa, bisa kaddamar da kashi na biyu na kungiyar NISCOPS a jihar, sannan Gwamnatin Jihar Kogi a shiye take wajen yin hadaka da kunyoyin Solidaridad da kuma IDH, domin amfana da karin wasu shiye-shiryensu, musamman don samar da sakamako mai matukar kyau.

“Bisa rattaba hannun yarjejeniyar da kananan hukumomi uku suka yi da wannan kungiya ta Solidaridad, kan shirin masu ruwa da tsaki na noman Kwakwar Manja na kasa (NISCOPS), hakan zai bai wa Jihar Kogi damar mayar da hankali, musamman a kan wannan fanni na noma; don samun gwaggwabar riba.

Folashade ta ci gaba da cewa, “Gwamnatin Kogi ta gode wa Gwamnatocin Kasashen Netherlands da kuma Ingila, kan dabbaka wannan shiri, musamman domin yaki da kalubalen sauyin yanayi, wanda hakan zai kara taimakawa wajen kara samar da wadataccen abinci; ba a jihar kadai ba, har da ma fadin kasa baki-daya.

Shi kuwa shugaban hukumar, Daan Wensing ya sanar da cewa; ana samun karin bukatar Manja, musamman saboda amfanin da yake da shi da kuma neman sa da ake yi a daukacin fadin duniya baki-daya.

Har wa yau kuma ya bayyana cewa, a karkashin shirin hadakar na NISCOPS da Solidariadad, kananan manoma ake bukata su amfana da shirin, ba wadanda suka ci suka tayar da kai ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
Ministan Niger: Kullum Niger Tana Daukar Sin a Matsayin Abokiyar Hadin Kanta Ta Farko

Ministan Niger: Kullum Niger Tana Daukar Sin a Matsayin Abokiyar Hadin Kanta Ta Farko

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.