• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Kogi Ta Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Noma Da Kungiyar Solidaridad

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Jihar Kogi Ta Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Noma Da Kungiyar Solidaridad
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kogi ta kulla yarjeniya da kungiyar aikin noma ta kasa da kasa (Solidaridad), don kara bunkasa fannin aikin noma da kuma kara samar da wadataccen abinci a jihar da ma kasa baki-daya.

Gwamnan Jihar, Ahmed Usman Ododo ne ya bayyana haka a lokacin kaddamar da aikin noma kashi na biyu da aka gudanar a babban birnin tarrayya Abuja.

  • Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin
  • Shettima Ya Ƙaddamar Da Ginin Ofishin Hukumar Raya Arewa Maso Gabas

Ododo ya bayyana hakan ne ta bakin Sakatariyar Gwamnatin Jihar, Dakta Folashade Arike Ayoade.

Har ila yau, ya bayyana cewa; gwamnatin tasa ta sha alwashin inganta

aikin noma a jihar, musamman duba da ganin yadda ta mallaki babbar gonar da ke garin Suleja a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

A cewar tata, Allah ya albarkaci jihar da dimbin damammaki a wannan bangare na aikin noma tare kuma da ingantacciyar kasar noman.

Har ila yau kuma, ta yaba wa kungiyar ta Solidaridad da kuma NIPCONS, bisa tunawa da jihar ta Kogi a bangaren aikin noma da suka yi.

Folashade ta kuma bayar da tabbacin mayar da hankalin gwamnatin jihar, wajen kara habaka fannin aikin noma a fadin jihar baki-daya.

Haka zalika, ta yaba wa Gwamnatocin Kasar Amurka da Netherlands; kan yin hadaka a kan shirin na habaka aikin noma na jihar.

Ta kara da cewa, babu shakka al’ummar jihar da dama sun amfana da ayyukan wannan kungiya ta NISCOPS.

Ta ci gaba da cewa, bisa kaddamar da kashi na biyu na kungiyar NISCOPS a jihar, sannan Gwamnatin Jihar Kogi a shiye take wajen yin hadaka da kunyoyin Solidaridad da kuma IDH, domin amfana da karin wasu shiye-shiryensu, musamman don samar da sakamako mai matukar kyau.

“Bisa rattaba hannun yarjejeniyar da kananan hukumomi uku suka yi da wannan kungiya ta Solidaridad, kan shirin masu ruwa da tsaki na noman Kwakwar Manja na kasa (NISCOPS), hakan zai bai wa Jihar Kogi damar mayar da hankali, musamman a kan wannan fanni na noma; don samun gwaggwabar riba.

Folashade ta ci gaba da cewa, “Gwamnatin Kogi ta gode wa Gwamnatocin Kasashen Netherlands da kuma Ingila, kan dabbaka wannan shiri, musamman domin yaki da kalubalen sauyin yanayi, wanda hakan zai kara taimakawa wajen kara samar da wadataccen abinci; ba a jihar kadai ba, har da ma fadin kasa baki-daya.

Shi kuwa shugaban hukumar, Daan Wensing ya sanar da cewa; ana samun karin bukatar Manja, musamman saboda amfanin da yake da shi da kuma neman sa da ake yi a daukacin fadin duniya baki-daya.

Har wa yau kuma ya bayyana cewa, a karkashin shirin hadakar na NISCOPS da Solidariadad, kananan manoma ake bukata su amfana da shirin, ba wadanda suka ci suka tayar da kai ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KogiKulla Yarjejeniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Djibouti Ya Baiwa Rukunin Tallafin Jinya Na Kasar Sin Karo Na 22 Lambar Yabo

Next Post

Ministan Niger: Kullum Niger Tana Daukar Sin a Matsayin Abokiyar Hadin Kanta Ta Farko

Related

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

6 days ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

6 days ago
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

3 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

3 weeks ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

3 weeks ago
Next Post
Ministan Niger: Kullum Niger Tana Daukar Sin a Matsayin Abokiyar Hadin Kanta Ta Farko

Ministan Niger: Kullum Niger Tana Daukar Sin a Matsayin Abokiyar Hadin Kanta Ta Farko

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.