ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Kogi Ta Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Noma Da Kungiyar Solidaridad

by Abubakar Abba
2 years ago
Kogi

Gwamnatin Jihar Kogi ta kulla yarjeniya da kungiyar aikin noma ta kasa da kasa (Solidaridad), don kara bunkasa fannin aikin noma da kuma kara samar da wadataccen abinci a jihar da ma kasa baki-daya.

Gwamnan Jihar, Ahmed Usman Ododo ne ya bayyana haka a lokacin kaddamar da aikin noma kashi na biyu da aka gudanar a babban birnin tarrayya Abuja.

  • Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin
  • Shettima Ya Ƙaddamar Da Ginin Ofishin Hukumar Raya Arewa Maso Gabas

Ododo ya bayyana hakan ne ta bakin Sakatariyar Gwamnatin Jihar, Dakta Folashade Arike Ayoade.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, ya bayyana cewa; gwamnatin tasa ta sha alwashin inganta

aikin noma a jihar, musamman duba da ganin yadda ta mallaki babbar gonar da ke garin Suleja a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

A cewar tata, Allah ya albarkaci jihar da dimbin damammaki a wannan bangare na aikin noma tare kuma da ingantacciyar kasar noman.

Har ila yau kuma, ta yaba wa kungiyar ta Solidaridad da kuma NIPCONS, bisa tunawa da jihar ta Kogi a bangaren aikin noma da suka yi.

Folashade ta kuma bayar da tabbacin mayar da hankalin gwamnatin jihar, wajen kara habaka fannin aikin noma a fadin jihar baki-daya.

Haka zalika, ta yaba wa Gwamnatocin Kasar Amurka da Netherlands; kan yin hadaka a kan shirin na habaka aikin noma na jihar.

Ta kara da cewa, babu shakka al’ummar jihar da dama sun amfana da ayyukan wannan kungiya ta NISCOPS.

Ta ci gaba da cewa, bisa kaddamar da kashi na biyu na kungiyar NISCOPS a jihar, sannan Gwamnatin Jihar Kogi a shiye take wajen yin hadaka da kunyoyin Solidaridad da kuma IDH, domin amfana da karin wasu shiye-shiryensu, musamman don samar da sakamako mai matukar kyau.

“Bisa rattaba hannun yarjejeniyar da kananan hukumomi uku suka yi da wannan kungiya ta Solidaridad, kan shirin masu ruwa da tsaki na noman Kwakwar Manja na kasa (NISCOPS), hakan zai bai wa Jihar Kogi damar mayar da hankali, musamman a kan wannan fanni na noma; don samun gwaggwabar riba.

Folashade ta ci gaba da cewa, “Gwamnatin Kogi ta gode wa Gwamnatocin Kasashen Netherlands da kuma Ingila, kan dabbaka wannan shiri, musamman domin yaki da kalubalen sauyin yanayi, wanda hakan zai kara taimakawa wajen kara samar da wadataccen abinci; ba a jihar kadai ba, har da ma fadin kasa baki-daya.

Shi kuwa shugaban hukumar, Daan Wensing ya sanar da cewa; ana samun karin bukatar Manja, musamman saboda amfanin da yake da shi da kuma neman sa da ake yi a daukacin fadin duniya baki-daya.

Har wa yau kuma ya bayyana cewa, a karkashin shirin hadakar na NISCOPS da Solidariadad, kananan manoma ake bukata su amfana da shirin, ba wadanda suka ci suka tayar da kai ba.

Kogi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
Noma Da Kiwo

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

June 12, 2026
Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
Noma Da Kiwo

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Next Post
Ministan Niger: Kullum Niger Tana Daukar Sin a Matsayin Abokiyar Hadin Kanta Ta Farko

Ministan Niger: Kullum Niger Tana Daukar Sin a Matsayin Abokiyar Hadin Kanta Ta Farko

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.