• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Kashe Mutum Shida Da Sace Wasu Ranar Sallah A Sokoto

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Sallah

Akalla mutane shida ne rahotanni suka ce an kashe tare da yin garkuwa da mutane sama da 100 yayin da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai wa wata al’umma hari a Jihar Sokoto.

Rundunar ‘yansanda sa Jihar Sokoto, ta bakin mai magana da yawunta, Ahmed Rufa’i, ta tabbatar da kashe mutum sama da 6 tare da yin garkuwa da dama a Tudun Doki da ke Karamar hukumar Gwadabawa a Sokoto.

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Kare Muhalli A Wuraren Kewayen Rawayen Kogi
  • Rashin Wadatar Kayan Aiki: Yadda Nijeriya Ta Kasa Dakatar Da Asarar Naira Tiriliyan 1.4 A Sashen Kiwon Lafiya

Rufa’i ya ce duk da cewa har yanzu ana tattara bayanai game da harin, amma an tabbatar da mutuwar mutum shida.

A cewarsa, jami’in ‘yansandan shiyya da ke Gwadabawa ya jagoranci tawagar ‘yansanda zuwa al’umma domin duba lamarin tare da dawo da zaman lafiya.

Akalla mutum shida ne rahotanni suka ce an kashe tare da yin garkuwa da mutane sama da 100 yayin da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai wa wata al’umma hari a Jihar Sokoto.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

“Rundunar bincike ta gano gawarwaki shida kuma ana ci gaba da kokarin kwato sauran mutanen da suka bata,” in ji kakakin ‘yansandan.

A cewar mazauna kauyen, maharan wadanda adadinsu ya kai kusan bakwai, sun far wa al’ummar da misalin karfe 1:30 na safe dauke da manyan bindigogi, sun harbin kan mai uwa da wabi inda suka yi awon gaba da ’yan uwa da dama.

Gwadabawa, daya daga cikin kananan hukumomin da ke Gundumar Sanata ta Gabas ta Jihar Sakkwato, ta kasance cikin kwanciyar hankali har zuwa harin da aka kai.

A halin da ake ciki dai sojojin Operation Whirl Punch sun ci gaba da kai samame tare da sintiri a Jihar Kaduna inda suka kashe wasu ‘yan bindiga uku a hanyar Gonna Rogo-Eka a Karamar Hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna.

Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida da Harkokin Gida Samuel Aruwan ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Majiyarmu ta ruwaito cewa, a ranar 14 ga watan Yuni, sojojin sun kashe ‘yan bindiga 36, ciki har da Buhari Alhaji Halidu, wanda aka fi sani da “Buharin Yadi,” daya daga cikin manyan ‘yan fashin da suka addabi Arewa.

Bayan kashe-kashen, mazauna yankunan kan iyakar Kaduna da Katsina sun shiga cikin farin ciki.

A wani samame na baya-bayan nan, kwamishinan ya ce, “Dakarun da ke aikin sintiri sun kashe ‘yan bindiga uku a yankin Gonna Rogo-Eka na Karamar Hukumar Kajuru.”

Ya kara da cewa an kwato bindigogin AK-47 guda biyu, kwanson AK-47 guda hudu da harsashi 81 na 7.62mm bayan wani kazamin fada aka gwabza da ‘yan fashin.

“Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce sojojin sun gudanar da sintiri na musamman a yankin inda suka samu ‘yan bindigar. Bayan musayar wuta, an kashe uku daga cikin masu laifin a takaice.

Gwamna Uba Sani, da yake magana a kan ci gaban, ya gode wa jami’an tsaro tare da yaba wa dakarun da ke karkashin jagorancin babban kwamandan runduna ta daya ta sojojin Nijeriya, Manjo Janar M.L.D Saraso, kan yadda suka kara kaimi wajen ganin an gudanar da bukukuwan Sallah lami lafiya. ‘yan kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Babban Burina Na Ga Ina Taimaka Wa Mata ‘Yan’uwana – Garkuwar Matan Giwa

Babban Burina Na Ga Ina Taimaka Wa Mata ‘Yan'uwana - Garkuwar Matan Giwa

LABARAI MASU NASABA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.