ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Kashe Mutum Shida Da Sace Wasu Ranar Sallah A Sokoto

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Sallah

Akalla mutane shida ne rahotanni suka ce an kashe tare da yin garkuwa da mutane sama da 100 yayin da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai wa wata al’umma hari a Jihar Sokoto.

Rundunar ‘yansanda sa Jihar Sokoto, ta bakin mai magana da yawunta, Ahmed Rufa’i, ta tabbatar da kashe mutum sama da 6 tare da yin garkuwa da dama a Tudun Doki da ke Karamar hukumar Gwadabawa a Sokoto.

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Kare Muhalli A Wuraren Kewayen Rawayen Kogi
  • Rashin Wadatar Kayan Aiki: Yadda Nijeriya Ta Kasa Dakatar Da Asarar Naira Tiriliyan 1.4 A Sashen Kiwon Lafiya

Rufa’i ya ce duk da cewa har yanzu ana tattara bayanai game da harin, amma an tabbatar da mutuwar mutum shida.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, jami’in ‘yansandan shiyya da ke Gwadabawa ya jagoranci tawagar ‘yansanda zuwa al’umma domin duba lamarin tare da dawo da zaman lafiya.

Akalla mutum shida ne rahotanni suka ce an kashe tare da yin garkuwa da mutane sama da 100 yayin da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai wa wata al’umma hari a Jihar Sokoto.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

“Rundunar bincike ta gano gawarwaki shida kuma ana ci gaba da kokarin kwato sauran mutanen da suka bata,” in ji kakakin ‘yansandan.

A cewar mazauna kauyen, maharan wadanda adadinsu ya kai kusan bakwai, sun far wa al’ummar da misalin karfe 1:30 na safe dauke da manyan bindigogi, sun harbin kan mai uwa da wabi inda suka yi awon gaba da ’yan uwa da dama.

Gwadabawa, daya daga cikin kananan hukumomin da ke Gundumar Sanata ta Gabas ta Jihar Sakkwato, ta kasance cikin kwanciyar hankali har zuwa harin da aka kai.

A halin da ake ciki dai sojojin Operation Whirl Punch sun ci gaba da kai samame tare da sintiri a Jihar Kaduna inda suka kashe wasu ‘yan bindiga uku a hanyar Gonna Rogo-Eka a Karamar Hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna.

Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida da Harkokin Gida Samuel Aruwan ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Majiyarmu ta ruwaito cewa, a ranar 14 ga watan Yuni, sojojin sun kashe ‘yan bindiga 36, ciki har da Buhari Alhaji Halidu, wanda aka fi sani da “Buharin Yadi,” daya daga cikin manyan ‘yan fashin da suka addabi Arewa.

Bayan kashe-kashen, mazauna yankunan kan iyakar Kaduna da Katsina sun shiga cikin farin ciki.

A wani samame na baya-bayan nan, kwamishinan ya ce, “Dakarun da ke aikin sintiri sun kashe ‘yan bindiga uku a yankin Gonna Rogo-Eka na Karamar Hukumar Kajuru.”

Ya kara da cewa an kwato bindigogin AK-47 guda biyu, kwanson AK-47 guda hudu da harsashi 81 na 7.62mm bayan wani kazamin fada aka gwabza da ‘yan fashin.

“Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce sojojin sun gudanar da sintiri na musamman a yankin inda suka samu ‘yan bindigar. Bayan musayar wuta, an kashe uku daga cikin masu laifin a takaice.

Gwamna Uba Sani, da yake magana a kan ci gaban, ya gode wa jami’an tsaro tare da yaba wa dakarun da ke karkashin jagorancin babban kwamandan runduna ta daya ta sojojin Nijeriya, Manjo Janar M.L.D Saraso, kan yadda suka kara kaimi wajen ganin an gudanar da bukukuwan Sallah lami lafiya. ‘yan kasa.

Sallah
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Babban Burina Na Ga Ina Taimaka Wa Mata ‘Yan’uwana – Garkuwar Matan Giwa

Babban Burina Na Ga Ina Taimaka Wa Mata ‘Yan'uwana - Garkuwar Matan Giwa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.