ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Kashe Mutum Shida Da Sace Wasu Ranar Sallah A Sokoto

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Sallah

Akalla mutane shida ne rahotanni suka ce an kashe tare da yin garkuwa da mutane sama da 100 yayin da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai wa wata al’umma hari a Jihar Sokoto.

Rundunar ‘yansanda sa Jihar Sokoto, ta bakin mai magana da yawunta, Ahmed Rufa’i, ta tabbatar da kashe mutum sama da 6 tare da yin garkuwa da dama a Tudun Doki da ke Karamar hukumar Gwadabawa a Sokoto.

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Kare Muhalli A Wuraren Kewayen Rawayen Kogi
  • Rashin Wadatar Kayan Aiki: Yadda Nijeriya Ta Kasa Dakatar Da Asarar Naira Tiriliyan 1.4 A Sashen Kiwon Lafiya

Rufa’i ya ce duk da cewa har yanzu ana tattara bayanai game da harin, amma an tabbatar da mutuwar mutum shida.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, jami’in ‘yansandan shiyya da ke Gwadabawa ya jagoranci tawagar ‘yansanda zuwa al’umma domin duba lamarin tare da dawo da zaman lafiya.

Akalla mutum shida ne rahotanni suka ce an kashe tare da yin garkuwa da mutane sama da 100 yayin da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai wa wata al’umma hari a Jihar Sokoto.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

“Rundunar bincike ta gano gawarwaki shida kuma ana ci gaba da kokarin kwato sauran mutanen da suka bata,” in ji kakakin ‘yansandan.

A cewar mazauna kauyen, maharan wadanda adadinsu ya kai kusan bakwai, sun far wa al’ummar da misalin karfe 1:30 na safe dauke da manyan bindigogi, sun harbin kan mai uwa da wabi inda suka yi awon gaba da ’yan uwa da dama.

Gwadabawa, daya daga cikin kananan hukumomin da ke Gundumar Sanata ta Gabas ta Jihar Sakkwato, ta kasance cikin kwanciyar hankali har zuwa harin da aka kai.

A halin da ake ciki dai sojojin Operation Whirl Punch sun ci gaba da kai samame tare da sintiri a Jihar Kaduna inda suka kashe wasu ‘yan bindiga uku a hanyar Gonna Rogo-Eka a Karamar Hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna.

Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida da Harkokin Gida Samuel Aruwan ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Majiyarmu ta ruwaito cewa, a ranar 14 ga watan Yuni, sojojin sun kashe ‘yan bindiga 36, ciki har da Buhari Alhaji Halidu, wanda aka fi sani da “Buharin Yadi,” daya daga cikin manyan ‘yan fashin da suka addabi Arewa.

Bayan kashe-kashen, mazauna yankunan kan iyakar Kaduna da Katsina sun shiga cikin farin ciki.

A wani samame na baya-bayan nan, kwamishinan ya ce, “Dakarun da ke aikin sintiri sun kashe ‘yan bindiga uku a yankin Gonna Rogo-Eka na Karamar Hukumar Kajuru.”

Ya kara da cewa an kwato bindigogin AK-47 guda biyu, kwanson AK-47 guda hudu da harsashi 81 na 7.62mm bayan wani kazamin fada aka gwabza da ‘yan fashin.

“Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce sojojin sun gudanar da sintiri na musamman a yankin inda suka samu ‘yan bindigar. Bayan musayar wuta, an kashe uku daga cikin masu laifin a takaice.

Gwamna Uba Sani, da yake magana a kan ci gaban, ya gode wa jami’an tsaro tare da yaba wa dakarun da ke karkashin jagorancin babban kwamandan runduna ta daya ta sojojin Nijeriya, Manjo Janar M.L.D Saraso, kan yadda suka kara kaimi wajen ganin an gudanar da bukukuwan Sallah lami lafiya. ‘yan kasa.

Sallah
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Babban Burina Na Ga Ina Taimaka Wa Mata ‘Yan’uwana – Garkuwar Matan Giwa

Babban Burina Na Ga Ina Taimaka Wa Mata ‘Yan'uwana - Garkuwar Matan Giwa

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.