• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Sun Roki Manyan Kasashen Duniya Su Kawo Musu Dauki 

by Sadiq
3 years ago
Fasinjoji

Ragowar fasinjojin da aka yi garkuwa da su a jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna sun yi kira ga manyan kasashen duniya da su taimaka su shiga tsakani a kan halin da suke ciki da kuma ganin an ceto su daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su.

Idan za a iya tunawa, ‘yan ta’adda sun kai wa jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna hari a daren ranar Litinin 28 ga watan Maris, 2022, inda fasinjoji tara suka mutu, sannan suka yi awon gaba da wasu da dama yayin da aka ceto wasu da dama da raunuka.

  • Me Ya Sa Kano Pillars Ta Fada Ajin Gajiyayyu A Nijeriya?
  • A Nijeriya Idan Ka Ce Za Ka Rike Aikin Gwamnati Shi Kadai Akwai Kalubale – Fatima (Adon Gari)

Mamu wanda ya jagoranci yin sulhu har aka sako mutane 18 daga cikin fasinjojin rukuni na biyu. Sun saki mutane 11 a ranar 11 ga Yuni, 2022, sai kuma suka sake sakin wani rukuni na fasinjojin bakwai a ranar 9 ga Yuli, 2022.

‘Yan ta’addan sun yi barazanar kashe sauran wadanda ke hannunsu, matukar gwamnatin tarayya ba ta biya musu bukatunsu ba, ciki har da bukatar sakin mayakansu da ake tsare da wadanda aka samu da laifi da kuma wadanda ke jiran hukuncin shari’a.

Daga bisani ‘yan ta’addan na Boko-Haram sun kai hari gidan yarin Kuje da ke Abuja, inda suka saki daruruwan fursunonin da suka hada da wasu 69 daga cikinsu da ke fuskantar tuhumar ta’addanci.

LABARAI MASU NASABA

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

Da yake mayar da martani kan harin, Mamu, ya sanar da janye wa daga tattaunawar neman sakin fasinjojin jirgin da aka sace, inda ya bayyana rashin kulawa daga gwamnatin tarayya ke nunawa da kuma barazana ga rayuwarsa da yake fuskanta.

Ya kuma zargi gwamnatin tarayya gaza yin katabus game da bayanan sirri kan yiwuwar harin na gidan yarin Kuje.

A wani sabon faifan bidiyo da ‘yan ta’addan suka fitar a ranar Asabar, wanda LEADERSHIP ta samu, an ga yadda ‘yan ta’addan ke yi wa wadanda aka yi garkuwa da su bulala, wadanda suka hada da manya maza da mata da kananan yara.

A cikin bidiyon mai tsawon mintuna 10.51, ‘yan ta’addan sun yi barazanar yin garkuwa da shugaban kasa Muhammadu Buhari da kuma gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai tare da kashe su.

‘Yan ta’addan sun kuma sha alwashin cewa za su ruguza kasar nan, su kashe sauran fasinjojin da ke hannunsu sannan su sayar da sauran.

Daya daga cikin ‘yan ta’addan ya yi barazanar cewa idan har gwamnati ba ta biya musu bukatunsu ba, to za su mayar da yankin tamkar mahauta.

“Wannan shi ne sakonmu ga gwamnatin Nijeriya kuma kamar yadda kuka ga wadannan mutane a nan, da yardar Allah za ku ga shugabanninku; Sanatoci da gwamnoninku za su zo gabanmu. Wadannan da kuke gani a nan za mu rike wasu a matsayin bayi, mu sayar da su kamar yadda Imaminmu ya fada muku a baya,” in ji shi.

Bayan ‘yan ta’addan sun yi magana, wasu daga cikin fasinjojin da aka sace sun roki gwamnatin tarayya da manyan kasashen duniya irin su; Faransa, Amurka, Ingila da sauransu da su kawo musu dauki.

Sun koka da halin da suke ciki tare da zargin gwamnati da rashin nuna kulawa, inda suka kara da cewa wadanda suka sace su sun fi mutunta su fiye da gwamnatin Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Manyan Labarai

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Kano
Manyan Labarai

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Next Post
Duk Abinda Na Yi A Rayuwata Bazata Ne – Obasanjo

Duk Abinda Na Yi A Rayuwata Bazata Ne - Obasanjo

LABARAI MASU NASABA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.