ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Abinda Na Yi A Rayuwata Bazata Ne – Obasanjo

by Sadiq
4 years ago
Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, a jiya ya bayyana cewa komai na rayuwarsa ya faru ne ta hanyar bazata wanda ya hada da zamansa a matsayin shugaban kasa a lokacin mulkin soja da kuma shugaban kasar Nijeriya a lokacin dimokuradiyya.

Tsohon shugaban kasar wanda ya zama bako na musamman a wani shiri na gidan rediyo mai zaman kansa a Abeokuta, ya ce in ban da noma da aka haife shi a ciki, wasu sun faru ne ta hanyar bazata, inda ya kara da cewa yana alfahari kasancewarsa manomi.

  • Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Sun Roki Manyan Kasashen Duniya Su Kawo Musu Dauki 
  • ‘Yan Sandan Birnin Milan Sun Ba Wa Dan Wasa Bukayoko Hakuri

Da yake amsa tambayoyi daga tsohon kyaftin din Super Eagles, Segun Odegbami, wanda ke jagorantar shirin Obasanjo ya jaddada cewa ba daidai ba ne kowa ya kira kansa manomi.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Ba na so kalmar da kuka yi amfani da ita, ‘ soyayya da noma’, ni manomi ne. Me kuke nufi da soyayya? Duk abin da na yi a rayuwata ta hanyar bazata ne. Abin da ba bazata bane, shi ne noma. Duk sauran abubuwan da na kasance cikin bazata ne.

“Ka san yadda na fara. An haife ni a kauye. Na je makaranta ne bisa bazata. Mahaifina ya ce, ‘ba za ku samar da komai na daban ba? Shi yasa na shiga harkar noma.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

“Idan aka duba kasashen da suka ci gaba, sun ci gaba ne a fannin noma. Na farko, don samar da abinci, na biyu don sarrafa abin da suke samu daga gonakinsu. Na uku, a ba da shi a matsayin fitar da shi zuwa kasashen waje, wanda shi ne manufar samun kudin waje.

“Kuma hanyar samar da ayyukan yi ne ga matasa”.

Obasanjo wanda ya shawarci matasan Nineriya da su karbi mukaman shugabanci a yanzu, ya bukace su da kada su bari wani ya yaudare su da sunan su manyan gobe ne.

Ya ce wasu gurbatattun shugabanni za su ruguza abin da ake kira gobe idan matasa suka kasa tashi tsaye su dauki makomarsu a hannunsu.

“Shawarata ga matasan Nijeriya ita ce, kada ku bari wani ya ce muku ku ne shugabannin gobe. Za ku jira goben kafin ku karbi ragamar shugabancin, to gobe ba za ta zo ba. Wannan lokaci ne da ya kamata matasa su tashi su tabbatar da hakan,” inji shi.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
De Ligt Ya Koma Bayern Munchen Daga Juventus

De Ligt Ya Koma Bayern Munchen Daga Juventus

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.