• English
  • Business News
Friday, July 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kenya Ya Kori Ministocin Kasar Baki Daya Daga Aiki

by Sadiq
1 year ago
in Kasashen Ketare
0
Shugaban Kenya Ya Kori Ministocin Kasar Baki Daya Daga Aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kenya William Ruto, ya sanar da korar dukkanin ministocinsa sakamakon boren da gwamnatinsa ta fuskanta daga jama’a saboda tsadar rayuwa.

A jawabin da ya yi wa al’ummar kasar ta kafar talabijin, Ruto ya ce wadanda korar ba ta shafa ba su ne mataimakin shugaban kasa Rigathi Gachagua da kuma ministan harkokin waje Musalia Mudavadi.

  • Badakalar Kudade Fiye Da Miliyan 37: Kotu A Kebbi Ta Umarce CSP Rano Ya Nemo Shaidun Kare Kansa
  • Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli Ta Ba Ƙananan Hukumomi ‘Yancin Cin Gashin Kansu

Al’ummar Kenya dai, sun kalubalanci gwamnatin kasar da rashin iya jagoranci, inda suka gudanar da zanga-zangar tsadar rayuwa da kuma ta adawa da sabon harajin da gwamnati ta yi shirin dora musu, har ta kai ga rasa rayuka.

Ana ta rade-radin cewa shugaban na shirin kafa wata sabuwar karamar gwamnati ne sakamakon zanga-zangar da aka kwashe makonni ana yi.

Shi dai, Ruto ya ce ya dauki wannan mataki ne bayan ya saurari jama’a, kuma nan take zai shiga tattaunawa mai zurfi a mabambantan bangarori da jam’iyyun siyasa da sauran al’ummar kasar domin kafa gwamnatin da za ta wakilci kowa da kowa.

Labarai Masu Nasaba

Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

Ya kara da cewa hakan ya zama wajibi ne domin hada karfi da karfe wajen kai wa kasar ga tudun mun tsira, sakamakon katutun matsalolin tattalin arziki da walwalar jama’a da suka dabaibaye ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KenyaMinistociTsadar RayuwaWilliam Ruto
ShareTweetSendShare
Previous Post

Albashi: Shugabannin Kungiyoyin Kwadago Na Gana Wa Da Tinubu A Abuja

Next Post

Sin Ta Gabatar Da Takardar Bayani Kan Yadda Take Kiyaye Muhallin Halittun Teku

Related

Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine
Kasashen Ketare

Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine

3 days ago
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari
Kasashen Ketare

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

4 days ago
Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba
Kasashen Ketare

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

5 days ago
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka
Kasashen Ketare

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

5 days ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Kasashen Ketare

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

5 days ago
Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan
Kasashen Ketare

Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan

2 weeks ago
Next Post
Sin Ta Gabatar Da Takardar Bayani Kan Yadda Take Kiyaye Muhallin Halittun Teku

Sin Ta Gabatar Da Takardar Bayani Kan Yadda Take Kiyaye Muhallin Halittun Teku

LABARAI MASU NASABA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dillalai Sun Rage Farashin Man Fetur A Nijeriya

July 18, 2025
Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum

Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum

July 18, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta

July 18, 2025
Nazari Game Da Rayuwar Muhammadu Buhari

Nazari Game Da Rayuwar Muhammadu Buhari

July 18, 2025
Wata Motar Tankar Mai Ta Kama Da Wuta Tare Da Kone Wasu Motoci A Ibadan, Jihar Oyo

Wata Motar Tankar Mai Ta Kama Da Wuta Tare Da Kone Wasu Motoci A Ibadan, Jihar Oyo

July 18, 2025
Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

July 18, 2025
'Yan Bindiga

Kaduna: An Horar Da Sarakunan Gargajiya Kan Sasanta Rikici Da Samar Da Zaman Lafiya

July 18, 2025
Rashin Halartar Gwamnoni Taron Yi Wa Tsarin Mulki Kwaskwarima A Kaduna Ya Haifar Da Cece-kuce

Rashin Halartar Gwamnoni Taron Yi Wa Tsarin Mulki Kwaskwarima A Kaduna Ya Haifar Da Cece-kuce

July 18, 2025
yola

Tinubu Ya Kammala Hanyoyi 420 A Sassan Nijeriya Cikin Shekara 2

July 18, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Tallafa Wa Yara Mata 8,225 Da Ke Sakandare

Gwamnan Zamfara Ya Tallafa Wa Yara Mata 8,225 Da Ke Sakandare

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.