• English
  • Business News
Thursday, August 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Za Mu Shiga Zanga-zangar Da Za A Yi Wa Tinubu Ba – Daliban Arewa

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
Ba Za Mu Shiga Zanga-zangar Da Za A Yi Wa Tinubu Ba – Daliban Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daliban Arewacin Najeriya sun janye daga shiga zanga-zangar gama-gari da ake shirin gudanarwa kan yunwa da tsadar rayuwa a kasar.

Daliban, karkashin gamayyar kungiyoyin dalibai masu kishin Arewa, sun sanar da janyewarsu ce ta wata wasika da Shugaban Majalisar Dattawa ta Kungiyar Daliban Jihar Kano ta Kasa (NAKS), Kwamred Jibrin Sani Bello.

  • Tinubu Ya Aike Wa Majalisa Takardar Neman Kara N6.2trn A Kasafin Kudin Bana
  • Shugaban Amurka, Joe Biden Ya Kamu Da Cutar Covid-19

Ya bayyana cewa sun yanke shawarar kaurace wa zanga-zangar ce saboda rashin sanin asalin wadanda suka shirya.

Kwamred Jibrin Sani Bello ya ce, “Shirye-shiryen zanga-zangar gama-garin sun riga sun yi nisa, amma bayan mun yi tuntuba da kuma zurfafa tunani, mun ga akwai buƙata daliban Najeriya sun kaurace wa zanga-zangar shiga ciki ta, da saboda rashin sanin wadanda suka shirya,” in ji shi.

Daliban sun bayyana cewa yawancin zanga-zangar da ake gudanarwa na kawo tsaiko ga harkokin karatunsu.

Labarai Masu Nasaba

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

Sun bayyana cewa duk da yake matsalar tsadar rayuwa ta addabi ’yan Najeriya, akwai bukatar a yi hattara kada a kara tsananta lamarin ta hanyar zanga-zanga mara kyakkyawan tsari.

“Mun yard yunwa da tsadar rayuwa sun addabi ’yan Najeriya, amma duk da haka akwai bukatar a yi hattara da shiga zanga-zangar da ba a san asalinta ba, wadda kuma ba a san irin mummunan sakamakon sa za ta haifar ba,” in ji Kwamred.

Sun bayyana zargin an saye wadanda suka shirya, shi ya sa kungiyoyin suka yanke shawarar kauracewa.

Maimakon zanga-zangar muna kira da a fadada shirin ba da tallafin karatu ga dalibai (NELFIND) ta yadda za a rika daukar nauyin daliban da suka cancanta su yi karatu a cikin gida da kasashen waje.

Wani dalibi a Jami’ar Umaru Musa Yar’adua da ke Katsina, Abdulrahman Mansir, ya ba da misali da wasu lokuta a baya inda zanga-zanga ta sa aka tsawaita zangon karatu da birkita jadawalin karatun dalibai.

“Dole mu tsara kanmu a matsayinmu na dalibai, saboda zanga-zanga na iya kawo cikas ga ci gaban iliminmu kuma ba zai magance matsalolin Najeriya ba.

“Za mu koma ga Allah Ya magance mana matsalolin kasarmu,” in ji Mansur.

Matasan a Nijeriya sun ta shirin fita zanga-zanga ta tsawon kwanaki 10, wadda za a fara a ranar 1 zuwa 10 ga watan Agustan 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalibaiDaliban ArewaTinubuTsadar RayuwaZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hasashen Ambaliyar Ruwa A Kano: Wane Shiri Gwamnati Da Jama’ar Gari Suka Yi?

Next Post

Ko Kun San Miliyan Nawa Gombe Ke Kashewa Don Tsaftace Jihar A Duk Wata?

Related

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara
Labarai

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

7 hours ago
APC
Labarai

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

9 hours ago
Tinubu
Labarai

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

10 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

12 hours ago
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

13 hours ago
NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano
Labarai

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

16 hours ago
Next Post
Ko Kun San Miliyan Nawa Gombe Ke Kashewa Don Tsaftace Jihar A Duk Wata?

Ko Kun San Miliyan Nawa Gombe Ke Kashewa Don Tsaftace Jihar A Duk Wata?

LABARAI MASU NASABA

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

August 13, 2025
Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.