ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Za Mu Shiga Zanga-zangar Da Za A Yi Wa Tinubu Ba – Daliban Arewa

by Sadiq
2 years ago
Daliban

Daliban Arewacin Najeriya sun janye daga shiga zanga-zangar gama-gari da ake shirin gudanarwa kan yunwa da tsadar rayuwa a kasar.

Daliban, karkashin gamayyar kungiyoyin dalibai masu kishin Arewa, sun sanar da janyewarsu ce ta wata wasika da Shugaban Majalisar Dattawa ta Kungiyar Daliban Jihar Kano ta Kasa (NAKS), Kwamred Jibrin Sani Bello.

  • Tinubu Ya Aike Wa Majalisa Takardar Neman Kara N6.2trn A Kasafin Kudin Bana
  • Shugaban Amurka, Joe Biden Ya Kamu Da Cutar Covid-19

Ya bayyana cewa sun yanke shawarar kaurace wa zanga-zangar ce saboda rashin sanin asalin wadanda suka shirya.

ADVERTISEMENT

Kwamred Jibrin Sani Bello ya ce, “Shirye-shiryen zanga-zangar gama-garin sun riga sun yi nisa, amma bayan mun yi tuntuba da kuma zurfafa tunani, mun ga akwai buƙata daliban Najeriya sun kaurace wa zanga-zangar shiga ciki ta, da saboda rashin sanin wadanda suka shirya,” in ji shi.

Daliban sun bayyana cewa yawancin zanga-zangar da ake gudanarwa na kawo tsaiko ga harkokin karatunsu.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Sun bayyana cewa duk da yake matsalar tsadar rayuwa ta addabi ’yan Najeriya, akwai bukatar a yi hattara kada a kara tsananta lamarin ta hanyar zanga-zanga mara kyakkyawan tsari.

“Mun yard yunwa da tsadar rayuwa sun addabi ’yan Najeriya, amma duk da haka akwai bukatar a yi hattara da shiga zanga-zangar da ba a san asalinta ba, wadda kuma ba a san irin mummunan sakamakon sa za ta haifar ba,” in ji Kwamred.

Sun bayyana zargin an saye wadanda suka shirya, shi ya sa kungiyoyin suka yanke shawarar kauracewa.

Maimakon zanga-zangar muna kira da a fadada shirin ba da tallafin karatu ga dalibai (NELFIND) ta yadda za a rika daukar nauyin daliban da suka cancanta su yi karatu a cikin gida da kasashen waje.

Wani dalibi a Jami’ar Umaru Musa Yar’adua da ke Katsina, Abdulrahman Mansir, ya ba da misali da wasu lokuta a baya inda zanga-zanga ta sa aka tsawaita zangon karatu da birkita jadawalin karatun dalibai.

“Dole mu tsara kanmu a matsayinmu na dalibai, saboda zanga-zanga na iya kawo cikas ga ci gaban iliminmu kuma ba zai magance matsalolin Najeriya ba.

“Za mu koma ga Allah Ya magance mana matsalolin kasarmu,” in ji Mansur.

Matasan a Nijeriya sun ta shirin fita zanga-zanga ta tsawon kwanaki 10, wadda za a fara a ranar 1 zuwa 10 ga watan Agustan 2024.

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Ko Kun San Miliyan Nawa Gombe Ke Kashewa Don Tsaftace Jihar A Duk Wata?

Ko Kun San Miliyan Nawa Gombe Ke Kashewa Don Tsaftace Jihar A Duk Wata?

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.