• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (4)

byIdris Aliyu Daudawa
1 year ago
Malaman

Kwalejin ilimi ba su yin abinda ya dace saboda ba a basu wani muhimmancin da ya kamata ba, hakan ma shi yasa lamarin koyarwa ya kasance wuri na karshe na wadanda suka kammala jami’a ba su kuma sha’awar aikin koyarwa,ba su kuma a shirya su koyi yadda za su koyar yadda ya dace.Domin kuwa suna yin aikin koyarwa ne kawai domin su samu hanyar biyan bukatunsu.

Shi ya sa masu makarantu ba shirye suke ba su rika basu albashin da ya dace ba,saboda yadda suka dauki malaman makaranta ba da wata daraja ba.Haka lamarin yake sai dai kuma ba a taru aka zama daya ba.

  • Sufeton ‘Yansanda Ya Amince Da Zanga-zangar Matsin Rayuwa, Ya Gindaya Sharadi
  • Muhimmin Sakon Kwankwaso Ga ‘Yan Nijeriya Kan Shirin Zanga-zanga 

Alalade ya kara yin bayani inda yake cewa rashin isassun malaman makaranta abin ba ya tsaya kadai bane kan Lissafi da Turanci,a takaice dukkan darussan.“Daga cikin ‘ya’yanmu namu muke son su zama malaman makaranta? Iyaye nawa suke fatan ‘ya’yansu su zama malaman makaranta? Makarantu nawa ko manyan makarantu suke koyarwa da manufar jan hankalin ‘yan makarantar su yi sha’awar aikin koyarwa?

Abin so ne a a daukaka darajar malaman makaranta ta kasance irin ta ma’aikatan Banki ko kuma masu aiki a kamfanin mai,domin yin hakan zai iya sa abubuwa  a canza yadda ake Kallon malaman makaranta, daga haka kuma za a fara ganin sauyi daga yadda suke gudanar da aikinsu.Muna sa ‘ya’yanmu amakaranta ne domin su yi aikin da bai danganta da koyarwa, idan kuma ba mu yi haka ba maganar karancin malamai a darussan Lissafi da Turanci abin zai kara kazancewa ne.Lukaci ya yi wanda dole ne sai mun canzawa matasa yadda ya dace da kamata su kaunaci aikin koyarwa da su malaman makaranta.

Kamata ya yi a fara yanzu domina sauya tunanin wasu dalibai su rungumi aikin koyarwa saboda a gaba a samu wadanda  za su yi aikin bilhakki da gaskiya.Dole ne a samo mafita na tsaro da wasu manufofin da sharuddan da za su jan hankalin wadanda basu sha’wara yin aikin malamain makaranta su yi sha’awar haka.Sai dai tambayar ita ce wanene, ko kuma me zai koyawa ‘ya’yanmu da jikokinmu  idan ba a yi tsarin da abin zai jawo hakali ba, ai zai wuyar ka tallata abinda ba ka tanada ba!”

LABARAI MASU NASABA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Iyaye da basu son ‘ya’yansu  su zama malaman makaranta

“Akwai abin da ke  bada gudunmawa wajen rashin isassun malaman da za su koyar a darussan Turanci da Lissafi. Abin mamaki shi ne iyaye na bukatar a koya wa ‘ya’yansu amma basu bukatar ‘ya’yansu su zama malaman makaranta.Ko wa ai ya san dalilin domin kuwa iyaye sun bar maida hankali a kan irin kokarin da ‘ya’yansu suke yi kamar yadda ya dace tun da farko su yi hakan.Ba su damu ba koma wanene zai koyawa ‘ya’yansu, su kawai abin da suke bukata ‘ya’yan su kasance sun samu zuwa ajin SS2.

Daga nan kuma sai ta wacce hanya ‘ya’yan nasu za su rubuta jarabawa sanin kowa ne kuma irin haka ne har sai aki ga  bata lokaci  saboda lokaci ya kure.Ya dace iyaye su maida hankali kamar yadda ya dace dangane da lamarin ilimin ‘ya’yansu.Su bada duk wata gudunmawar da suka za ta taimaka wajen ilimin da ‘ya’yansu za su samu mai nagarta,matukar idan har basu bukatar a rika ba ‘ya’yansu duk abin da aka ga dama da suna albashi,idan ba fata da bukatar kaiwa ga haka, a kula da malaman makaranta wajen biyansu albashi mafi tsoka ta haka ne ‘ya’yanku da jikokinsu za su samu ilimi mai inganci.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta
Ilimi

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya
Ilimi

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Next Post
Amfanin Hulba 21 Ga Lafiyar Dan’adam (2)

Amfanin Almiski Da Sabulunsa (2)

LABARAI MASU NASABA

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version