ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimmin Sakon Kwankwaso Ga ‘Yan Nijeriya Kan Shirin Zanga-zanga 

Da Karfin Kuri'a Za Mu Iya Magance Matsalolin Nijeriya 

by Sulaiman
2 years ago
Kwankwaso

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bukaci ‘yan Nijeriya da su nemi sauyi ta hanyar dimokuradiyya maimakon zanga-zanga.

 

A wata sanarwa da shi da kan sa ya sanya wa hannu a ranar Juma’a 26 ga Yuli, 2024 a cikin mawuyaciyar rayuwa da ake ciki da kuma kiraye-kirayen nuna adawa da halin da ake ciki ta hanyar zanga-zanga, Sanata Kwankwaso ya jaddada cewa, za a iya samun sauyi mai inganci kuma mai dorewa ta hanyar karfin zabe.

ADVERTISEMENT

 

“Da tsananin nauyin da ya rataya akaina nake bayyana ra’ayina game da halin da ake ciki a kasarmu Nijeriya, mun tsinci kanmu cikin wahalhalun da ba za a iya gujewa ba saboda shugabanninmu sun rasa wasu matakai tun 2007,” in ji

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

 

A ko da yaushe, lokacin gyara ba ya kurewa, za a iya dora kasar nan kan turba mai kyau don bunkasar tattalin arziki, wadata, da kyautata jin dadin ‘yan kasa.

 

Kwankwaso ya bayyana wasu rigingimu da suka samo asali daga rashin shugabanci na gari, kamar “yadda gwamnatin tarayya ta yi katsalandan a harkokin masarautun jihar Kano, da tsige mataimakin gwamnan jihar Edo, da rudanin siyasa a jihar Ribas, da rashin tsaro da ya addabi kasar nan baki daya.

 

“Sauran sun hada da rikicin siyasa a Jihar Kogi, zagon kasa ga matatar mai ta AIiko Dangote, takaddama game da yarjejeniyar auren jinsi (SAMOA), rikici tsakanin Sanata Ali Ndume da Shugabannin APC. Duk wadannan katsalandan ba dole ba ne, za a iya kauce musu.”

 

Ya kara da cewa, wadannan al’amura alamu ne na rashin bin ka’ida da kuma nuna gaskiya.

 

“Abin bakin ciki ne yadda rashin shugabanci na gari da son kai na shugabanni ya jefa ‘yan kasa musamman matasa cikin yunwa da rashin tsaro da kuma yanke kyakkyawan tsammani ga kasar.” in ji Kwankwaso.

 

Don haka, ya yi kira ga shugabannin Nijeriya a dukkan matakai da su gaggauta magance wadannan kalubale ta hanyar tabbatar da kyakkyawan shugabanci da bin doka da oda.

 

Da yake amincewa da kiraye-kirayen zanga-zangar da aka yi a baya-bayan nan, Kwankwaso ya amince da bacin rai da kuma burin ganin Nijeriya ta gyaru amma ya ja kunne kan illar da hakan zai iya haifarwa.

 

Ya bukaci ‘yan Nijeriya da su yi amfani da karfin kuri’unsu a matsayin makami mafi inganci wajen kawo sauyi.

Kwankwaso
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Next Post
Amfanin Hulba 21 Ga Lafiyar Dan’adam (2)

Amfanin Hulba 21 Ga Lafiyar Dan’adam (2)

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.