ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Matawalle Ce Ta Rura Wutar Ta’addanci A Arewa – Turji

by Sulaiman
1 year ago
Matawalle

Wani kasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, da ke ta’addanci a arewacin Nijeriya, ya zargi karamin ministan tsaro kuma tsohon Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, da rashin kula da lamarin sulhu da ‘yan bindiga yadda ya kamata a lokacin da yake gwamnan jihar.

 

A lokacin da yake gwamna, Matawalle ya kaddamar da shirin yin afuwa ga ‘yan bindiga inda ya bayyana tattaunawa a matsayin mafi kyawun zabi na magance ta’addancin ‘yan bindiga.

ADVERTISEMENT
  • Jihar Kano Na Shirin Gudanar Da Zaben Ƙananan Hukumomi – Gwamna Abba
  • Shugaba Tinubu Ya Mika Sakon Ta’aziyya ga Kasar Vietnam Kan Rasuwar Nguyễn Phú Trọng

Sai dai kuma daga baya ya janye afuwar, yana mai cewa ‘yan bindigar sun gaza rungumar shirin zaman lafiyar da gwamnatinsa ta yi musu.

 

LABARAI MASU NASABA

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

A cikin wani faifan bidiyo da aka saki a shafukan sada zumunta kuma Daily Trust ta nakalto, Turji ya alakanta karuwar ta’addanci a Zamfara da sauran jihohin Arewa maso Yamma kan manufofin da Matawalle ya tsara a lokacin da yake gwamna.

 

“Duk mutumin da ke zaune a Shinkafi, Zurmi, da Isa (Jihar Sokoto) ba zai iya musanta wannan ikirari ba. Akwai wasu gungun ‘yan bindiga da suka zama ‘yan lelen tsohon gwamnan. Na kore su daga Shinkafi, na kashe shugabansu, Dudu, domin samun dawwamammen zaman lafiya a Shinkafi. Kungiyar na da makamai 200, amma daga baya gwamnan ya karbe su (Yaran Dudu) a gidan gwamnati.

 

“Kuma gwamnati ta gaza nemansu (Yaran Dudu) da su mika makamansu. Sannan akwai Wata kungiya da Bashari Maniya ke jagoranta tana da bindigogi sama da 300.”

 

Turji ya yi ikirarin cewa, ya kwace bindigu 30 daga hannun sansanin ‘yan bindigar da ke karkashin jagorancin Bashari Maniya, kuma kungiyar ba ta taba mika makamanta ga gwamnati ba.

 

A cikin faifan bidiyon, Turji ya kuma yi zargin cewa, wasu shugabannin kungiyoyin ‘yan bindiga da ke cikin yarjejeniyar zaman lafiya da gwamnatin Matawalle ta kaddamar sun koma Sokoto da zama bayan sun bai wa yaransu makamai domin ci gaba da yin garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

 

“Ali yaro ne ga Kabiru Maniya, kuma shi ne ke da alhakin kai hare-hare a yankin Tangaza. Bashiri da Kabiru duk suna zaune ne a cikin babban birnin Sokoto, suna jin dadin rayuwarsu. Akwai Wani Buhari, shi ma yana cikin garin Sokoto yana jin dadin rayuwarsa.

 

“Makonni uku da suka wuce, an kama wani kanin Buhari da bindigogi a cikin babban birnin Sokoto. Babu mai musanta wannan. Zan iya fitowa da hujjojin bidiyo wanda ke nuna yadda Kabiru Maniya ke harba manyan bindigogi.

 

“Abin tambaya a yanzu shi ne, ina bindigoginsu bayan da suka ce sun rungumi zaman lafiya sun zauna a garin Sokoto?

 

Ya dace gwamnati ta bayyana wa ’yan Nijeriya wanda ke da alhakin kashe jama’a. Su daina zargin Bello Turji da kashe-kashe da garkuwa da mutane.

 

“Mutanen da ake garkuwa da su a cikin babban birnin Sokoto aka kai su bayan Achida da Goronyo, wa ke da alhakin yin garkuwa da su? Har yanzu Bello Turji ne ? Wanda yake zaune lafiya a Shinkafi?

 

Kokarin jin ta bakin Matawalle domin jin ta bakinsa ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

 

Kiraye-kiraye da yawa da aka yi wa Henshaw Ogubike, mai magana da yawun ma’aikatar tsaro, ya ci tura.

 

Ogbuike, ya aika da sakon tes, inda ya nemi wakilin Daily trust ya yi masa bayanin kiran ta hanyar rubutu (tes) amma bai mayar da martani ga sakon da aka aika masa ba har zuwa lokacin rubuta wannan rahoton.

 

A baya dai Matawalle ya musanta alaka da ‘yan bindigar, ya kuma kara da cewa, gwamnatinsa ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin ta magance matsalolin tsaro a Zamfara a lokacin da yake kan mulki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

November 12, 2025
Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna
Manyan Labarai

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Next Post
An Kama Wanda Ya Kitsa Kashe Janar Udokwere A Kano

An Kama Wanda Ya Kitsa Kashe Janar Udokwere A Kano

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

November 12, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

November 12, 2025
Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

November 12, 2025
Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.