• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CMG Ya Gudanar Da Tattaunawa Kan “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya” A kasashen Najeriya Da Afirka Ta Kudu Da Zambiya

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
CMG

A ran 25 ga wata, an gudanar da tattaunawa kan “Zurfafa gyare-gyare a Sin dama ce ga duniya” a cibiyar al’adun kasar Sin dake birnin Abuja a Najeriya, wanda rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin CMG da cibiyar raya al’adu ta kasar Sin suka shirya. Taron ya jawo manyan baki da masana wadanda suka gabatar da fahimta mai zurfi game da gyare-gyaren da kasar Sin ke yi da kuma tasirinsu a duniya.

 

An bude taron ne da jawabin mataimakin ministan yada manufofin JKS, kuma shugaban CMG Mista Shen Haixiong, inda ya jaddada muhimmancin ci gaba da yin hadin gwiwa tare da nuna godiya ga mahalarta taron.

  • Masana Sun Bayyana Alfanun Manufar Gyare-gyaren Kasar Sin A Sabon Zamani A Abuja
  • Sin Ta Shawarci Kasashen Da Suka Mallaki Makaman Nukiliya Kada Su Yi Amfani Da Shi Wajen Kaiwa Juna Hari 

Muhimman jawabai sun hada da bayani mai zurfi kan tasirin kasar Sin ga tattalin arzikin duniya, da muhimmiyar gudummawar da take bayarwa ga yanayin tattalin arzikin Najeriya daga bakin malama Fa’iza Mustapha. Yayin da Misis Patricia Naria, wacce ta wakilci mai girma ministan ma’aikatar yawon bude ido ta tarayya Najeriya, ta mayar da hankali kan bunkasa harkokin yawon bude ido a Najeriya da karfafa gwiwar matasa domin dakile kaura daga karkara zuwa birane.

 

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Taron ya kasance dandalin tattaunawa da mu’amala mai karfi, inda ya bayyana irin gyare-gyaren da kasar Sin ke aiwatarwa, da tasirinsu a duniya, wanda ya nuna muhimmancin ci gaba da yin hadin gwiwa tsakanin Sin da Najeriya, wajen cimma muradun ci gaba na bai daya.

 

Bugu da kari, a ranar 24 ga watan Yuli agogon kasar Afirka ta Kudu, CMG ta gudanar da irin wannan taro a birnin Johannesburg, inda shugaban CMG Shen Haixiong ya gabatar da jawabi ta kafar bidiyo.

 

Shen Haixiong ya bayyana cewa, kwanan nan aka yi nasarar kammala cikakken zama karo na uku na kwamitin kolin JKS karo na 20 a birnin Beijing, wanda ya jawo hankalin duniya baki daya.

 

Wannan wani gagarumin ci gaba ne ga kasar Sin a sabon zamani. CMG ya himmatu wajen ba da labaran gyare-gyaren kasar Sin da bude kofa ga waje, da ba da labaran zamanantarwa irin ta kasar Sin, da yin aiki tukuru wajen gina gada ta cudanya da mu’amala, da tattaunawa, da fahimtar juna, da tuntubar juna tsakanin Sin da kasashen duniya.

 

Kazalika a wannan rana, CMG ya yi nasarar gudanar da taron tattaunawar a birnin Lusaka na kasar Zambiya. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
Next Post
Wasu Ɓata-gari Na Iya Amfani Da Zanga-zanga Domin Tada Zaune Tsaye – Minista

Wasu Ɓata-gari Na Iya Amfani Da Zanga-zanga Domin Tada Zaune Tsaye - Minista

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.