ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Bayyana Alfanun Manufar Gyare-gyaren Kasar Sin A Sabon Zamani A Abuja

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
gyare

A yau Alhamis aka gudanar da wani taron ƙara wa juna sani a Cibiyar Al’adun Kasar Sin da ke Babban Birnin Tarayya Abuja mai taken “Gyare-gyaren kasar Sin a Sabon Zamani”.

Taron wanda aka gudanar bisa hadin gwiwar cibiyar al’adun da Hukumar Kafofin Watsa Labarai ta Kasar Sin (CMG) ta samu halartar kwararru da manyan baki wadanda suka yi karin haske a kan gyare-gyaren da kasar Sin ta tsunduma yi da kuma alfanunsu ga al’ummar duniya.

An fara taron ne da gabatar da jawabin Mataimakin Daraktan Sashen Yada Labarai na Kwamitin Tsakiya na Jam’iyyar CPC kuma Darakta Janar na Hukumar Kafofin Watsa Labarai ta Kasar Sin, Mista Shen, inda ya nuna muhimmancin dorewar hadin gwiwa tare da mika godiya ga mahalarta taron.
Mista Shen, ya jaddada wajibcin hadin kai a tsakanin al’ummomin duniya domin cimma muradun ci gaba da kowa da kowa ke hankoron gani.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, masu gabatar da jawabai daban-daban a wurin taron sun yi gamsassun bayanai game da rawar da kasar Sin ke takawa wajen taimaka wa ci gaban kasashen duniya.

Musamman wacce ta yi fashin baki a kan tasirin da kasar Sin ke yi wajen bunkasa tattalin arzikin duniya, Fa’iza Muhammed, ta ce ba karamar gudunmawa kasar Sin ta bayar wajen daidaita turbar habakar tattalin arzikin Nijeriya ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

A nata bangaren, wakiliyar Ministar Bunkasa Yawon Bude, Misis Patricia Naria, ta mayar da hankali ne a kan yadda za a ciyar da harkokin yawon bude ido gaba a Nijeriya, kana ta nemi a karfafa matasa domin takaita kwararar mutane daga kauyuka zuwa birane.
Shi kuwa, Mista Raphael Oni, ya yi bayani ne a kan abubuwan da za a iya cimmawa idan aka samu hadin gwiwa da inganta kwazon aiki tsakanin kasashen duniya, kana ya yi tsokaci a kan irin rawar da Sin ke takawa wajen samar da ma’aikata a sassa daban-daban na ci gaban Nijeriya.

Shugaban Kungiyar ‘Yan Nijeriya Da Suka Samu Horo a Kasar Sin, Malam Mohammed Sulaiman, ya yi karin haske a kan muradun ci gaban kasa da Sin ta sanya a gaba da kuma kokarin da take yi na zamanantar da harkokinta tare da tabbatar da dorewar bunkasar duniya da zurfafa ci gaban kimiyya.

Daga bangaren Mista Okon Emmanuel kuwa, ya nuna muhimmancin shigar da matasa ne cikin harkokin yawon bude ido domin a dama da su, yayin da ita kuma Edi-ima Ekpety ta yi bayyana abubuwa masu ban sha’awa da ta koya a kasar Sin lokacin da take karatu a can inda ta nuna alfanun sanin al’adun juna da kuma damammakin karo ilimi da ake samu.
An dai kammala taron ne da jawabin mai gabatar da taron wanda ya nuna muhimmancin abubuwan da baki masu gabatar da jawabai suka bayyana tare da daukar hotuna da ke nuna sabunta hadin kai da zumunci a tsakanin mahalarta taron.

  • Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin APC Kan Zanga-zangar Matsin Rayuwa

Za a iya cewa taron na kara wa juna sani da aka gabatar, ya samar da wata kafa ta tattaunawa da musanyar ra’ayoyi da kuma Karin haske a kan manufar gyare-gyaren da Sin ke yi da yadda abin zai amfanar da duniya tare da jaddada muhimmancin hadin gwiwa a tsakanin Nijeriya da Sin domin a gudu tare a tsira tare.

gyare
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
CMG Ya Gudanar Da Tattaunawa Kan “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya” A kasashen Najeriya Da Afirka Ta Kudu Da Zambiya

CMG Ya Gudanar Da Tattaunawa Kan “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya” A kasashen Najeriya Da Afirka Ta Kudu Da Zambiya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.