• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-zanga: Kebbi Ta Bukaci Matasa Da Su Guji Tashe-tashen Hankula

by Sulaiman and Umar Faruk
10 months ago
in Labarai
0
Zanga-zanga: Kebbi Ta Bukaci Matasa Da Su Guji Tashe-tashen Hankula
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani kakkausan kira na wanzar da zaman lafiya, Shugaban Ma’aikatan jihar Kebbi, Alhaji Sifiyanu Garba Bena, ya bukaci matasa da ma’aikata a Nijeriya da su guji shiga ayyukan ‘yan daba a yayin gudanar da zanga-zangar da ake shirin gudanar wa a fadin Nijeriya.

 

Da yake jawabi ga manema labarai a safiyar ranar Alhamis a ofishinsa da ke Birnin Kebbi, Shugaban ma’aikatan jihar, Alhaji Sifiyanu Garba Bena ya jaddada cewa, duk da cewa zanga-zangar lumana hakki ne da tsarin mulki ya tanada, amma bai kamata a yi barna ko tada fitina a tsakanin al’umma ba.

  • Zanga-zanga-zanga: Tinubu Ya Yi Taron Gaggawa Da Manyan Sarakunan Gargajiya A Abuja
  • Zanga-zangar Matsin Rayuwa: Gwamnoni Sun Gana Da Ribadu Kan Sha’anin Tsaro

“Mun amince da mutunta ‘yancin matasanmu na bayyana damuwarsu ta hanyar zanga-zangar lumana, amma muna yin Allah-wadai da duk wani nau’i na tashin hankali, lalata dukiyoyin jama’a ko ta gwamnati, da duk wani aiki da zai iya rikidewa zuwa rikici tsakanin al’umma.” In ji Bena

 

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Wannan kiran  na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun tashe-tashen hankula bayan zanga-zangar baya-bayan nan da ta rikide zuwa tashe tashen hankula, lamarin da ya janyo hasarar dimbin ababen more rayuwa na gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu.

 

Don haka, ana kara nuna damuwa kan illar da ka iya haifar da tarzoma ga zaman lafiya da hadin kan al’umma a fadin Nijeriya.

 

Alhaji Sifiyanu Garba Bena ya bukaci masu ruwa da tsaki musamman wadanda suka shirya zanga-zangar da su ba da fifiko wajen fadin albarkacin bakinsu tare da kaucewa ayyukan da za su kawo cikas ga tsaro da zamantakewar al’umma a jahohin Nijeriya.

 

Ya kuma tabbatar wa da jama’a cewa jami’an tsaro sun shirya tsaf domin kare lafiyar jama’a tare da mutunta ‘yancin ‘yan kasa.

 

“Muna aiki kafada da kafada da jami’an tsaro domin ganin an samar da isassun matakan kare rayuka da dukiyoyi a yayin zanga-zangar,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaRashin TsaroTabarbarewar IlimiTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawan Hatsi Da Sin Ta Samu Ya Zarce Kg Biliyan 650 Cikin Shekaru 9 A Jere

Next Post

Sin Na Ci Gaba Da Ingiza Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

5 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

6 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

7 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

9 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

10 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

11 hours ago
Next Post
Sin Na Ci Gaba Da Ingiza Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Ingiza Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.