• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Bayero Ta Fito Da Kurakuran Da Ake Tafkawa A Rediyo Da Talabijin

by Mustapha Ibrahim
1 year ago
in Ilimi
0
BUK
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An fito da kura-kuren da ake samu wajen fassarawa ko rubuta labarai a gidajen rediyo da telbijin na kasar nan a taron da cibiyar nazarin harsunan Nijeriya ta Jami’ar Bayero karkashin shugabancin Farfesa Yakubu Magaji Azare.

 

An dai gudanar da taron ne a harabar tsohowar jami’ar Bayero da ke Jihar Kano.

  • Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin APC Kan Zanga-zangar Matsin Rayuwa
  • Ƴancin Gashin Kai: Gwamnati Ta Gargadi Ƙananan Hukumomi Kan Kashe Kuɗaɗensu

Taron ya samu halartar masu ruwa da tsaki kan fassara, malaman jami’a, ma’aikatan gidan rediyo, ‘yan jaridu da kuma masu fassara a kotunan shari’ar kasar nan, domin inganta al’amuran fassara a wannan lokaci.

 

Labarai Masu Nasaba

Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

Taken taron dai shi ne, “Nasarori da kalubalen fassara”, wanda aka tattauna lamarin domin lalubo hanyar samun ingantaciyar fassara da ya kamata a rika yi a hanyoyin sadarwa na rediyo da talbijin, wanda a nan ne aka fi samun kura-kurai sabanin jaridu da suke kokari wajen yin kyakkywar fassara da kaucewa kura-kurai kamar yadda ake samu a rediyo da talbijin.

 

A jawabinsa, masanin harshen Hausa, Farfesa Hafiz Miko Yakasai yana da ra’ayin a daina kiran gidajen rediyo da talbijin da jarida da sauransu a matsayin kafofin watsa labarai, don haka hanyoyin sadarwa shi ne, wanda ake yin daidai a fahimtarsa da ra’ayinsa a matsayinsa na farfesa a harshen Hausa.

 

Shi kuwa ma’aikacin gidan rediyon Premier, Malam Aliyu Abubakar Getso, ya ce akwai kura-kurai masu yawa da ake yi wajen fassara ko rubuta labarai, inda ya ba da misisali da wasu ‘yan jarida masu cewa, ‘‘yan takarkaru’, wanda kuskure ne sai dai a ce, ‘yan takara, shi ne daidai.

 

Shi ma tsohon shugaban kungiyar ‘yan jaridu na kasa kuma shugaban gidan rediyon Nasara, Malam Ismail Mai Zare, ya ce kuskure ne babba da masu fassara ko ‘yan jaridu ke yi wajen ba da labari ka ji an ce filin sauka da tashin jirgin sama na Malam Aminu Kano, ko na Murtala Muhammad, maimakon a ce filin saukar jirgin sama shi ne daidai.

 

A nasa bangaren, Farfesa Abdullah Uba, (FYD) ya ce wajibi ne a rika la’akari da harshen da mutanan gari suke yi da sauran bayanan matasa, musamman rubutu a kafofin sadarwa na zamani wato ‘Social Media’ da sauransu.

 

Malam Abubakar Adamu Rano, shi ne shugaban gidan rediyon Kano mafi dadewa a tsakanin gidajen rediyon Arewa, wanda aka kafa a 1946, ya ce su a matsayinsu na masu kyankyashe ma’aikatan rediyo da ake da su sama da 30 a Kano, to suna taka-tsantsan sosai na ganin sun bi ka’idojin aikin fassara da rubuta labari kamar yadda masana a wannan cibiya ta Jami’ar Bayero suke ilmantarwa.

 

Tun da farko a jawabinsa, mataimakin shugaban jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Farfesa Sani Muhammad Gumel ya bayyana cewa wannan taro abin farinciki ne kuma abun a yaba wa mahalartansa ne.

 

Ya ce ya kamata a sani cewa jami’a ba wurin karatu ba ne kawai, jami’a wani muhimmin wuri ne na canza rayuwar al’umma, don haka ne ma Jami’ar Bayero ta kasance mai cibiyoyi daban-daban kamar na CDA cibiya mai bincike kan gano iri da sauran abun da zai bunkasa harkokin noma dan samar da abinci a kasa ga kuma cibiya mai kula da al’amuran lafiya da dai sauransu a jami’ar.

 

Shugaban cibiyar nazarin harsunan Nijeriya na jami’ar Bayero, Farfesa Yakubu Magaji Azare ya ce dole ne mai fassara ya yi la’akari da al’adu da addini da shekaru mutane da sauransu.

 

Ya ce fassara ta kasu kasha-kashi, akwai fassara ta lokaci, akwai fassara nan take da dai sauransu, sannan a ilimance kuma wannan cibiya ta sha alkashin fito da dinbin rubuce-rubucen da aka yi na fassara na masana daban-daban da cibiyar take jibge, haka kuma a kwai yunkuri na shirya wani gagarimun taro wanda zai hada daukacin masu ruwa da tsaki kamar ‘yan jaridu, masana, malaman addini da sauransu, domin fito da gundarin harkar fassara ingantaciya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ABUATBUBUK
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Da Amurka Sun Jaddada Kudurin Karfafa Kasuwanci A Tsakaninsu

Next Post

Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Gogewarta Ga Kasashen Afrika

Related

Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima
Ilimi

Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima

7 days ago
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah
Ilimi

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

3 weeks ago
Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya
Ilimi

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya

3 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

4 weeks ago
‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato
Ilimi

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

1 month ago
UTME
Ilimi

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

1 month ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Gogewarta Ga Kasashen Afrika

Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Gogewarta Ga Kasashen Afrika

LABARAI MASU NASABA

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.