ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Bayero Ta Fito Da Kurakuran Da Ake Tafkawa A Rediyo Da Talabijin

by Mustapha Ibrahim
2 years ago
BUK

An fito da kura-kuren da ake samu wajen fassarawa ko rubuta labarai a gidajen rediyo da telbijin na kasar nan a taron da cibiyar nazarin harsunan Nijeriya ta Jami’ar Bayero karkashin shugabancin Farfesa Yakubu Magaji Azare.

 

An dai gudanar da taron ne a harabar tsohowar jami’ar Bayero da ke Jihar Kano.

ADVERTISEMENT
  • Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin APC Kan Zanga-zangar Matsin Rayuwa
  • Ƴancin Gashin Kai: Gwamnati Ta Gargadi Ƙananan Hukumomi Kan Kashe Kuɗaɗensu

Taron ya samu halartar masu ruwa da tsaki kan fassara, malaman jami’a, ma’aikatan gidan rediyo, ‘yan jaridu da kuma masu fassara a kotunan shari’ar kasar nan, domin inganta al’amuran fassara a wannan lokaci.

 

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Taken taron dai shi ne, “Nasarori da kalubalen fassara”, wanda aka tattauna lamarin domin lalubo hanyar samun ingantaciyar fassara da ya kamata a rika yi a hanyoyin sadarwa na rediyo da talbijin, wanda a nan ne aka fi samun kura-kurai sabanin jaridu da suke kokari wajen yin kyakkywar fassara da kaucewa kura-kurai kamar yadda ake samu a rediyo da talbijin.

 

A jawabinsa, masanin harshen Hausa, Farfesa Hafiz Miko Yakasai yana da ra’ayin a daina kiran gidajen rediyo da talbijin da jarida da sauransu a matsayin kafofin watsa labarai, don haka hanyoyin sadarwa shi ne, wanda ake yin daidai a fahimtarsa da ra’ayinsa a matsayinsa na farfesa a harshen Hausa.

 

Shi kuwa ma’aikacin gidan rediyon Premier, Malam Aliyu Abubakar Getso, ya ce akwai kura-kurai masu yawa da ake yi wajen fassara ko rubuta labarai, inda ya ba da misisali da wasu ‘yan jarida masu cewa, ‘‘yan takarkaru’, wanda kuskure ne sai dai a ce, ‘yan takara, shi ne daidai.

 

Shi ma tsohon shugaban kungiyar ‘yan jaridu na kasa kuma shugaban gidan rediyon Nasara, Malam Ismail Mai Zare, ya ce kuskure ne babba da masu fassara ko ‘yan jaridu ke yi wajen ba da labari ka ji an ce filin sauka da tashin jirgin sama na Malam Aminu Kano, ko na Murtala Muhammad, maimakon a ce filin saukar jirgin sama shi ne daidai.

 

A nasa bangaren, Farfesa Abdullah Uba, (FYD) ya ce wajibi ne a rika la’akari da harshen da mutanan gari suke yi da sauran bayanan matasa, musamman rubutu a kafofin sadarwa na zamani wato ‘Social Media’ da sauransu.

 

Malam Abubakar Adamu Rano, shi ne shugaban gidan rediyon Kano mafi dadewa a tsakanin gidajen rediyon Arewa, wanda aka kafa a 1946, ya ce su a matsayinsu na masu kyankyashe ma’aikatan rediyo da ake da su sama da 30 a Kano, to suna taka-tsantsan sosai na ganin sun bi ka’idojin aikin fassara da rubuta labari kamar yadda masana a wannan cibiya ta Jami’ar Bayero suke ilmantarwa.

 

Tun da farko a jawabinsa, mataimakin shugaban jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Farfesa Sani Muhammad Gumel ya bayyana cewa wannan taro abin farinciki ne kuma abun a yaba wa mahalartansa ne.

 

Ya ce ya kamata a sani cewa jami’a ba wurin karatu ba ne kawai, jami’a wani muhimmin wuri ne na canza rayuwar al’umma, don haka ne ma Jami’ar Bayero ta kasance mai cibiyoyi daban-daban kamar na CDA cibiya mai bincike kan gano iri da sauran abun da zai bunkasa harkokin noma dan samar da abinci a kasa ga kuma cibiya mai kula da al’amuran lafiya da dai sauransu a jami’ar.

 

Shugaban cibiyar nazarin harsunan Nijeriya na jami’ar Bayero, Farfesa Yakubu Magaji Azare ya ce dole ne mai fassara ya yi la’akari da al’adu da addini da shekaru mutane da sauransu.

 

Ya ce fassara ta kasu kasha-kashi, akwai fassara ta lokaci, akwai fassara nan take da dai sauransu, sannan a ilimance kuma wannan cibiya ta sha alkashin fito da dinbin rubuce-rubucen da aka yi na fassara na masana daban-daban da cibiyar take jibge, haka kuma a kwai yunkuri na shirya wani gagarimun taro wanda zai hada daukacin masu ruwa da tsaki kamar ‘yan jaridu, masana, malaman addini da sauransu, domin fito da gundarin harkar fassara ingantaciya.

Bayero
Mustapha Ibrahim
+ postsBio
  • Mustapha Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/mustapha-ibrahim/
    Ma’aikatar REMASAB Ta Ƙaddamar Da Shirin Aikin Mai Da Shara Taki A Kano
  • Mustapha Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/mustapha-ibrahim/
    Cire Alamar PDP A Zaben Jihohi Biyu Ta Sa Sardauna Ya Nemo Wa Mabiyansa Mafita —Farfesa Sule Yau
  • Mustapha Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/mustapha-ibrahim/
    An Ƙirƙiro Da Shirin ‘Kano First’ Ne Don Sanya Wa Kanawa Kishin Jiharsu —Bala Gwagwarwa
  • Mustapha Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/mustapha-ibrahim/
    Idan Gwamna Abba Ya Ziyarci Kwalejin Bebeji Matsalarmu Za Ta Zo Ƙarshe – HOD Habib

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Gogewarta Ga Kasashen Afrika

Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Gogewarta Ga Kasashen Afrika

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.