• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Bayero Ta Fito Da Kurakuran Da Ake Tafkawa A Rediyo Da Talabijin

by Mustapha Ibrahim
12 months ago
in Ilimi
0
BUK
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An fito da kura-kuren da ake samu wajen fassarawa ko rubuta labarai a gidajen rediyo da telbijin na kasar nan a taron da cibiyar nazarin harsunan Nijeriya ta Jami’ar Bayero karkashin shugabancin Farfesa Yakubu Magaji Azare.

 

An dai gudanar da taron ne a harabar tsohowar jami’ar Bayero da ke Jihar Kano.

  • Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin APC Kan Zanga-zangar Matsin Rayuwa
  • Ƴancin Gashin Kai: Gwamnati Ta Gargadi Ƙananan Hukumomi Kan Kashe Kuɗaɗensu

Taron ya samu halartar masu ruwa da tsaki kan fassara, malaman jami’a, ma’aikatan gidan rediyo, ‘yan jaridu da kuma masu fassara a kotunan shari’ar kasar nan, domin inganta al’amuran fassara a wannan lokaci.

 

Labarai Masu Nasaba

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Taken taron dai shi ne, “Nasarori da kalubalen fassara”, wanda aka tattauna lamarin domin lalubo hanyar samun ingantaciyar fassara da ya kamata a rika yi a hanyoyin sadarwa na rediyo da talbijin, wanda a nan ne aka fi samun kura-kurai sabanin jaridu da suke kokari wajen yin kyakkywar fassara da kaucewa kura-kurai kamar yadda ake samu a rediyo da talbijin.

 

A jawabinsa, masanin harshen Hausa, Farfesa Hafiz Miko Yakasai yana da ra’ayin a daina kiran gidajen rediyo da talbijin da jarida da sauransu a matsayin kafofin watsa labarai, don haka hanyoyin sadarwa shi ne, wanda ake yin daidai a fahimtarsa da ra’ayinsa a matsayinsa na farfesa a harshen Hausa.

 

Shi kuwa ma’aikacin gidan rediyon Premier, Malam Aliyu Abubakar Getso, ya ce akwai kura-kurai masu yawa da ake yi wajen fassara ko rubuta labarai, inda ya ba da misisali da wasu ‘yan jarida masu cewa, ‘‘yan takarkaru’, wanda kuskure ne sai dai a ce, ‘yan takara, shi ne daidai.

 

Shi ma tsohon shugaban kungiyar ‘yan jaridu na kasa kuma shugaban gidan rediyon Nasara, Malam Ismail Mai Zare, ya ce kuskure ne babba da masu fassara ko ‘yan jaridu ke yi wajen ba da labari ka ji an ce filin sauka da tashin jirgin sama na Malam Aminu Kano, ko na Murtala Muhammad, maimakon a ce filin saukar jirgin sama shi ne daidai.

 

A nasa bangaren, Farfesa Abdullah Uba, (FYD) ya ce wajibi ne a rika la’akari da harshen da mutanan gari suke yi da sauran bayanan matasa, musamman rubutu a kafofin sadarwa na zamani wato ‘Social Media’ da sauransu.

 

Malam Abubakar Adamu Rano, shi ne shugaban gidan rediyon Kano mafi dadewa a tsakanin gidajen rediyon Arewa, wanda aka kafa a 1946, ya ce su a matsayinsu na masu kyankyashe ma’aikatan rediyo da ake da su sama da 30 a Kano, to suna taka-tsantsan sosai na ganin sun bi ka’idojin aikin fassara da rubuta labari kamar yadda masana a wannan cibiya ta Jami’ar Bayero suke ilmantarwa.

 

Tun da farko a jawabinsa, mataimakin shugaban jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Farfesa Sani Muhammad Gumel ya bayyana cewa wannan taro abin farinciki ne kuma abun a yaba wa mahalartansa ne.

 

Ya ce ya kamata a sani cewa jami’a ba wurin karatu ba ne kawai, jami’a wani muhimmin wuri ne na canza rayuwar al’umma, don haka ne ma Jami’ar Bayero ta kasance mai cibiyoyi daban-daban kamar na CDA cibiya mai bincike kan gano iri da sauran abun da zai bunkasa harkokin noma dan samar da abinci a kasa ga kuma cibiya mai kula da al’amuran lafiya da dai sauransu a jami’ar.

 

Shugaban cibiyar nazarin harsunan Nijeriya na jami’ar Bayero, Farfesa Yakubu Magaji Azare ya ce dole ne mai fassara ya yi la’akari da al’adu da addini da shekaru mutane da sauransu.

 

Ya ce fassara ta kasu kasha-kashi, akwai fassara ta lokaci, akwai fassara nan take da dai sauransu, sannan a ilimance kuma wannan cibiya ta sha alkashin fito da dinbin rubuce-rubucen da aka yi na fassara na masana daban-daban da cibiyar take jibge, haka kuma a kwai yunkuri na shirya wani gagarimun taro wanda zai hada daukacin masu ruwa da tsaki kamar ‘yan jaridu, masana, malaman addini da sauransu, domin fito da gundarin harkar fassara ingantaciya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ABUATBUBUK
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Da Amurka Sun Jaddada Kudurin Karfafa Kasuwanci A Tsakaninsu

Next Post

Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Gogewarta Ga Kasashen Afrika

Related

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate
Ilimi

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

4 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

6 days ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

2 weeks ago
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima
Ilimi

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

3 weeks ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Gogewarta Ga Kasashen Afrika

Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Gogewarta Ga Kasashen Afrika

LABARAI MASU NASABA

Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.