• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Hanyar Kara Zurfafa Gyare-gyare Sin Da Sauran Sassan Duniya Za Su Cimma Manyan Nasarori

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ta Hanyar Kara Zurfafa Gyare-gyare Sin Da Sauran Sassan Duniya Za Su Cimma Manyan Nasarori
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani rahoton baya bayan nan da manyan masana da masu ruwa da tsaki a kasar Sin suka fitar, ya fayyace alkiblar da kasar ta sanya gaba, da salon ta na aiwatar da muhimman manufofin gyare-gyare a gida.

 

Rahoton mai taken “Kara zurfafa cikakkun sauye-sauye domin ingiza zamanantarwa irin ta Sin: Cimma manyan nasarori da gudummawa ga sauran sassan duniya”, ya fayyace matakan Sin na cimma nasarar aiwatar da gyare-gyare a gida daga dukkanin fannoni, da irin tasirin da hakan zai yi ga ci gaban duniya baki daya.

  • Shugaban Zanzibar Ta Tanzania: Ba Za Iya Raba Ci Gaban Afirka Da Sin Ba
  • Kasar Sin Tana Da Likitocin Kauyuka Miliyan 1.1

Zamanantarwa irin ta kasar Sin manufa ce da za ta haifar da sabon salon ci gaba ga burin dan Adam na samun bunkasuwa da wayewar kai. Musamman duba da cewa tun shekaru da dama da suka gabata, sassan yammacin duniya ke burin cimma nasarar hakan bisa salo na jarin hujja, har ma wasu kasashe na ganin salo daya tilo da zai kai ga samar da nasara ga bil adama shi ne bin matakan wayewar kai irin na yammacin duniya, yayin da jarin hujja ke zama hanya daya tak ta raya tattalin arziki.

To sai dai kuma sabanin hakan, ta hanyar mayar da hankali ga irin kwarewa, da darussa da Sin ta koya a tafarkinta na neman ci gaba, muna iya ganin yadda Sin din ke kara tattara dabaru, da fasahohin zurfafa gyare gyare daga dukkanin fannoni, inda tuni kasar ta cimma nasarar kama hanyar zamanintarwa wadda ta sabawa ta kasashen yammacin duniya kuma mai cike da nasarori.

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Manufofin gyare-gyare a gida da bude kofa ga waje na Sin, sun zamo kan gaba a turbar da kasar ke bi ta zamanintar da kai. Kasar Sin na aiki tukuru wajen bunkasa tattalin arziki, wanda hakan ya haifar da bunkasar ma’aunin GDPn ta, har ta kai matsayin ta biyu a duniya ta fuskar karfin tattalin arziki. Cikin shekaru kusan 10, Sin ta yi nasarar tsame mutane kimanin miliyan 100 daga kangin talauci, yayin da adadin Sinawa masu matsakaicin samun kudin shiga ya haura miliyan 400, adadin da ya zamo irinsa na daya a duniya.

A kan wannan sabuwar hanyan neman ci gaba, kasar Sin na nacewa bude kofa domin ingiza nasarar sauye-sauye, da fadada hadin gwiwa tsakanin sassan kasa da kasa, da gina sabbin sassa, domin daga matsayin budadden tattalin arzikinta zuwa matsayin koli, matakin da ko shakka babu zai ci gaba da haifar da gajiya, da alherai masu yawa ga ita kanta Sin din da ma sauran sassan duniya. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shin Da Gaske NNPC Na Ba Wa Dangote Mai, Cikakken Bayani

Next Post

PDP Ta Shafta Karya, Ba Mu Da Wata Alaƙa Da APC – KESIEC

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

13 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

14 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

16 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

16 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

18 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

20 hours ago
Next Post
PDP Ta Shafta Karya, Ba Mu Da Wata Alaƙa Da APC – KESIEC

PDP Ta Shafta Karya, Ba Mu Da Wata Alaƙa Da APC - KESIEC

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.