• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Hanyar Kara Zurfafa Gyare-gyare Sin Da Sauran Sassan Duniya Za Su Cimma Manyan Nasarori

by Sulaiman and CGTN Hausa
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Ta Hanyar Kara Zurfafa Gyare-gyare Sin Da Sauran Sassan Duniya Za Su Cimma Manyan Nasarori
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani rahoton baya bayan nan da manyan masana da masu ruwa da tsaki a kasar Sin suka fitar, ya fayyace alkiblar da kasar ta sanya gaba, da salon ta na aiwatar da muhimman manufofin gyare-gyare a gida.

 

Rahoton mai taken “Kara zurfafa cikakkun sauye-sauye domin ingiza zamanantarwa irin ta Sin: Cimma manyan nasarori da gudummawa ga sauran sassan duniya”, ya fayyace matakan Sin na cimma nasarar aiwatar da gyare-gyare a gida daga dukkanin fannoni, da irin tasirin da hakan zai yi ga ci gaban duniya baki daya.

  • Shugaban Zanzibar Ta Tanzania: Ba Za Iya Raba Ci Gaban Afirka Da Sin Ba
  • Kasar Sin Tana Da Likitocin Kauyuka Miliyan 1.1

Zamanantarwa irin ta kasar Sin manufa ce da za ta haifar da sabon salon ci gaba ga burin dan Adam na samun bunkasuwa da wayewar kai. Musamman duba da cewa tun shekaru da dama da suka gabata, sassan yammacin duniya ke burin cimma nasarar hakan bisa salo na jarin hujja, har ma wasu kasashe na ganin salo daya tilo da zai kai ga samar da nasara ga bil adama shi ne bin matakan wayewar kai irin na yammacin duniya, yayin da jarin hujja ke zama hanya daya tak ta raya tattalin arziki.

To sai dai kuma sabanin hakan, ta hanyar mayar da hankali ga irin kwarewa, da darussa da Sin ta koya a tafarkinta na neman ci gaba, muna iya ganin yadda Sin din ke kara tattara dabaru, da fasahohin zurfafa gyare gyare daga dukkanin fannoni, inda tuni kasar ta cimma nasarar kama hanyar zamanintarwa wadda ta sabawa ta kasashen yammacin duniya kuma mai cike da nasarori.

Labarai Masu Nasaba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Manufofin gyare-gyare a gida da bude kofa ga waje na Sin, sun zamo kan gaba a turbar da kasar ke bi ta zamanintar da kai. Kasar Sin na aiki tukuru wajen bunkasa tattalin arziki, wanda hakan ya haifar da bunkasar ma’aunin GDPn ta, har ta kai matsayin ta biyu a duniya ta fuskar karfin tattalin arziki. Cikin shekaru kusan 10, Sin ta yi nasarar tsame mutane kimanin miliyan 100 daga kangin talauci, yayin da adadin Sinawa masu matsakaicin samun kudin shiga ya haura miliyan 400, adadin da ya zamo irinsa na daya a duniya.

A kan wannan sabuwar hanyan neman ci gaba, kasar Sin na nacewa bude kofa domin ingiza nasarar sauye-sauye, da fadada hadin gwiwa tsakanin sassan kasa da kasa, da gina sabbin sassa, domin daga matsayin budadden tattalin arzikinta zuwa matsayin koli, matakin da ko shakka babu zai ci gaba da haifar da gajiya, da alherai masu yawa ga ita kanta Sin din da ma sauran sassan duniya. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shin Da Gaske NNPC Na Ba Wa Dangote Mai, Cikakken Bayani

Next Post

PDP Ta Shafta Karya, Ba Mu Da Wata Alaƙa Da APC – KESIEC

Related

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba
Daga Birnin Sin

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

18 hours ago
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

18 hours ago
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

19 hours ago
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

20 hours ago
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

21 hours ago
Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

22 hours ago
Next Post
PDP Ta Shafta Karya, Ba Mu Da Wata Alaƙa Da APC – KESIEC

PDP Ta Shafta Karya, Ba Mu Da Wata Alaƙa Da APC - KESIEC

LABARAI MASU NASABA

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.