• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Zuwan Mbappe Zai Dusashe Tauraruwar Bellingham A Real Madrid?

by Abba Ibrahim Wada
12 months ago
in Wasanni
0
Ko Zuwan Mbappe Zai Dusashe Tauraruwar Bellingham A Real Madrid?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan cikar burin shugaban kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid na kawo dan wasa Kylian Mbappe, rahotanni da masu sharhi suka fara bayyana cewa magoya baya da shugabannin kungiyar za su karkatar da soyayyar da suke yi wa Jude Bellingham zuwa Mbappe, matakin da kociyan kungiyar, Carlo Ancelotti ya bayyana a matsayin shaci fadi kuma matsayin Bellingham a Real Madrid ba zai canza ba a bana, bayan daukar Kylian Mbappe.

Bellingham, dan wasan Ingila, mai shekara 21, ya taka rawar gani a Sifaniya a kakarsa ta farko, wanda ya zura kwallo 23 a wasanni 42 kuma yana cikin ‘‘yan wasan da suka taka rawar gani a Real Madrid, wacce ta lashe La Liga da Champions League a kakar da ta wuce.

  • Muna Samun Nasarori A Yaki Da Gurbatattun Masana’antar Kannywood – Tijjani Asase
  • Matasa Sun Yi Warwason Motar Taki A Adamawa

Mbappe, kyaftin din tawagar Faransa, mai shekara 25, ya koma Real Madrid a bana daga Paris St Ger-main, bayan da kwantiraginsa ya kare a watan Yuni kuma tuni ya koma Real Madrid bayan kammala gasar cin kofin Nahiyar Turai.

Ancelotti ya yi watsi da batun cewa Bellingham ba zai dinga buga gurbin da ya saba bugawa a Real Ma-drid ba, domin bai wa Mbappe dama, kociyan dan kasar Italiya ya bayyana cewa babu wani abu da zai canza a gare shi.

“Kakar farko, ya bai wa mutane mamaki, saboda yadda ya nuna kwarewa, yanzu kuma ya kara samun gogewa. Kenan wannan kakar haka zai ci gaba da taka rawar gani kuma zai ci gaba da zama fitatcen dan wasan wannan kungiya, wanda zai ci gaba da taka rawar da kungiyar za ta ci gaba da samun nasarori,” in ji Ancelotti

Labarai Masu Nasaba

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Ancelotti ya goyi da bayan Bellingham, wanda aka rika sukar kwazonsa a Euro 2024, duk da cewar Ingila ta kai wasan karshe a gasar kuma ya ce wannan ra’ayinsa ne, amma Bellingham ya taka rawar gani sosai a gasar cin kofin Zakarun Turai ta Euro 2024.

Sai dai ba iya shugabannin Real Madrid ba ne ake ganin za su mayar da Mbappe dan lele, magoya bayan kungiyar ma ana ganin za su karkata ga Mbappe, kasancewar sun dade suna fatan ganin ya koma kungiyar.

Amma ana ganin ba iya Bellingham da Mbappe bane za a samu wannan cece kucen, dan wasa Binicius ma ana ganin yana bukatar goyon bayan magoya baya da shugabanni saboda nauyin da yake kansa a kungiyar a yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BellinghamMbappeReal Madrid
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsarin Shayar Da Jarirai Da Sauran Sauye-sauyen Da Aka Samu A Gasar Olympics

Next Post

Gwamna Yusuf Ya Jaddada Ƙudirinsa Na Yaƙi Da Cin Hanci Da Rashawa A Kano

Related

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu
Wasanni

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

32 minutes ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

15 hours ago
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
Wasanni

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

1 day ago
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

4 days ago
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

5 days ago
Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo
Wasanni

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo

5 days ago
Next Post
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Jaddada Ƙudirinsa Na Yaƙi Da Cin Hanci Da Rashawa A Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.