• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Zuwan Mbappe Zai Dusashe Tauraruwar Bellingham A Real Madrid?

by Abba Ibrahim Wada
10 months ago
in Wasanni
0
Ko Zuwan Mbappe Zai Dusashe Tauraruwar Bellingham A Real Madrid?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan cikar burin shugaban kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid na kawo dan wasa Kylian Mbappe, rahotanni da masu sharhi suka fara bayyana cewa magoya baya da shugabannin kungiyar za su karkatar da soyayyar da suke yi wa Jude Bellingham zuwa Mbappe, matakin da kociyan kungiyar, Carlo Ancelotti ya bayyana a matsayin shaci fadi kuma matsayin Bellingham a Real Madrid ba zai canza ba a bana, bayan daukar Kylian Mbappe.

Bellingham, dan wasan Ingila, mai shekara 21, ya taka rawar gani a Sifaniya a kakarsa ta farko, wanda ya zura kwallo 23 a wasanni 42 kuma yana cikin ‘‘yan wasan da suka taka rawar gani a Real Madrid, wacce ta lashe La Liga da Champions League a kakar da ta wuce.

  • Muna Samun Nasarori A Yaki Da Gurbatattun Masana’antar Kannywood – Tijjani Asase
  • Matasa Sun Yi Warwason Motar Taki A Adamawa

Mbappe, kyaftin din tawagar Faransa, mai shekara 25, ya koma Real Madrid a bana daga Paris St Ger-main, bayan da kwantiraginsa ya kare a watan Yuni kuma tuni ya koma Real Madrid bayan kammala gasar cin kofin Nahiyar Turai.

Ancelotti ya yi watsi da batun cewa Bellingham ba zai dinga buga gurbin da ya saba bugawa a Real Ma-drid ba, domin bai wa Mbappe dama, kociyan dan kasar Italiya ya bayyana cewa babu wani abu da zai canza a gare shi.

“Kakar farko, ya bai wa mutane mamaki, saboda yadda ya nuna kwarewa, yanzu kuma ya kara samun gogewa. Kenan wannan kakar haka zai ci gaba da taka rawar gani kuma zai ci gaba da zama fitatcen dan wasan wannan kungiya, wanda zai ci gaba da taka rawar da kungiyar za ta ci gaba da samun nasarori,” in ji Ancelotti

Labarai Masu Nasaba

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Ancelotti ya goyi da bayan Bellingham, wanda aka rika sukar kwazonsa a Euro 2024, duk da cewar Ingila ta kai wasan karshe a gasar kuma ya ce wannan ra’ayinsa ne, amma Bellingham ya taka rawar gani sosai a gasar cin kofin Zakarun Turai ta Euro 2024.

Sai dai ba iya shugabannin Real Madrid ba ne ake ganin za su mayar da Mbappe dan lele, magoya bayan kungiyar ma ana ganin za su karkata ga Mbappe, kasancewar sun dade suna fatan ganin ya koma kungiyar.

Amma ana ganin ba iya Bellingham da Mbappe bane za a samu wannan cece kucen, dan wasa Binicius ma ana ganin yana bukatar goyon bayan magoya baya da shugabanni saboda nauyin da yake kansa a kungiyar a yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BellinghamMbappeReal Madrid
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsarin Shayar Da Jarirai Da Sauran Sauye-sauyen Da Aka Samu A Gasar Olympics

Next Post

Gwamna Yusuf Ya Jaddada Ƙudirinsa Na Yaƙi Da Cin Hanci Da Rashawa A Kano

Related

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona
Wasanni

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

1 day ago
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Wasanni

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

3 days ago
Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

5 days ago
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa
Wasanni

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

6 days ago
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano
Labarai

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

7 days ago
Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica
Wasanni

Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

7 days ago
Next Post
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Jaddada Ƙudirinsa Na Yaƙi Da Cin Hanci Da Rashawa A Kano

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.