ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Zuwan Mbappe Zai Dusashe Tauraruwar Bellingham A Real Madrid?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Mbappe

Tun bayan cikar burin shugaban kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid na kawo dan wasa Kylian Mbappe, rahotanni da masu sharhi suka fara bayyana cewa magoya baya da shugabannin kungiyar za su karkatar da soyayyar da suke yi wa Jude Bellingham zuwa Mbappe, matakin da kociyan kungiyar, Carlo Ancelotti ya bayyana a matsayin shaci fadi kuma matsayin Bellingham a Real Madrid ba zai canza ba a bana, bayan daukar Kylian Mbappe.

Bellingham, dan wasan Ingila, mai shekara 21, ya taka rawar gani a Sifaniya a kakarsa ta farko, wanda ya zura kwallo 23 a wasanni 42 kuma yana cikin ‘‘yan wasan da suka taka rawar gani a Real Madrid, wacce ta lashe La Liga da Champions League a kakar da ta wuce.

  • Muna Samun Nasarori A Yaki Da Gurbatattun Masana’antar Kannywood – Tijjani Asase
  • Matasa Sun Yi Warwason Motar Taki A Adamawa

Mbappe, kyaftin din tawagar Faransa, mai shekara 25, ya koma Real Madrid a bana daga Paris St Ger-main, bayan da kwantiraginsa ya kare a watan Yuni kuma tuni ya koma Real Madrid bayan kammala gasar cin kofin Nahiyar Turai.

ADVERTISEMENT

Ancelotti ya yi watsi da batun cewa Bellingham ba zai dinga buga gurbin da ya saba bugawa a Real Ma-drid ba, domin bai wa Mbappe dama, kociyan dan kasar Italiya ya bayyana cewa babu wani abu da zai canza a gare shi.

“Kakar farko, ya bai wa mutane mamaki, saboda yadda ya nuna kwarewa, yanzu kuma ya kara samun gogewa. Kenan wannan kakar haka zai ci gaba da taka rawar gani kuma zai ci gaba da zama fitatcen dan wasan wannan kungiya, wanda zai ci gaba da taka rawar da kungiyar za ta ci gaba da samun nasarori,” in ji Ancelotti

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Ancelotti ya goyi da bayan Bellingham, wanda aka rika sukar kwazonsa a Euro 2024, duk da cewar Ingila ta kai wasan karshe a gasar kuma ya ce wannan ra’ayinsa ne, amma Bellingham ya taka rawar gani sosai a gasar cin kofin Zakarun Turai ta Euro 2024.

Sai dai ba iya shugabannin Real Madrid ba ne ake ganin za su mayar da Mbappe dan lele, magoya bayan kungiyar ma ana ganin za su karkata ga Mbappe, kasancewar sun dade suna fatan ganin ya koma kungiyar.

Amma ana ganin ba iya Bellingham da Mbappe bane za a samu wannan cece kucen, dan wasa Binicius ma ana ganin yana bukatar goyon bayan magoya baya da shugabanni saboda nauyin da yake kansa a kungiyar a yanzu.

Mbappe
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
Wasanni

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Next Post
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Jaddada Ƙudirinsa Na Yaƙi Da Cin Hanci Da Rashawa A Kano

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.