• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gasar Olympics Na Kyautata Abota, Da Inganta Makomar Bai daya

by Sulaiman and CGTN Hausa
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Gasar Olympics Na Kyautata Abota, Da Inganta Makomar Bai daya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sau da dama mu kan nakalto Pierre de Coubertin, wanda ya kafa kwamitin Olympics na kasa da kasa kuma aka fi sani da uban wasannin Olympics na zamani, inda ya ce, “Shiga gasar wasannin Olympics ya fi lashe gasar muhimmanci, saboda muhimmin abu a rayuwa ba shi ne yin nasara ba, amma yin fafutuka cike da kwarin gwiwa shi ne nasara. Yada wadannan ka’idoji na karfafa gwiwa, da jarumta, da gina bil Adama mai kishi da karimci.” Tabbas wannan batu haka yake, saboda gasar wasannin Olympics ta dade da sauya manufarta ta zakulo mafi kyawun ‘yan wasa a duniya, yanzu ta zama dandalin cudanyar bil’adama, bege da mafarkai, da zaman lafiya da hadin kai. Wasanni gaba daya, musamman wasannin Olympics, na hada kan jama’a ba tare da la’akari da bambancin matsayi na shugabanci, ko siyasa ko addini ba. Kasar Faransa ce ta karbi bakunci gasar Olympics ta bana wadda ta gudana daga ranar 25 ga Yuli zuwa ta 11 ga Agusta. ’Yan wasa sun fafata tsakaninsu cike da kauna da kishin kasashensu a zuciya yayin da suka yi cudanya da takwarorinsa cikin nishadi da annushwa.

 

Bana ce ta cika shekaru 60 da kulla huldar diflomasiya tsakanin Sin da Faransa, kuma gasar wasannin Olympic ta sake ba da damammaki ga kasashen biyu wajen karfafa dankon zumuncin dake tsakaninsu, kuma ta yin hakan, za su sa kaimi ga yin hadin gwiwa bisa la’akari da muhimmancin samun ci gaba a duniya. A kwanakin da suka biyo bayan bikin bude gasar, mun ga sakonni da dama a kafar yanar gizo daga abokai na kasar Sin wadanda suka yaba da gagarumin gudummawa da kasar Sin ta bayar ga nasarar bikin a birnin Paris.

 

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana ruhin Olympics a yayin da ya kai ziyara kasar Faransa a watan Mayun shekarar 2024, domin halartar bikin rufe taro karo na shida na kwamitin ‘yan kasuwa na Sin da Faransa, inda ya ce, yana kallon wasannin Paris a matsayin wata dama ga kasashen biyu wajen zurfafa dangantakarsu ta tarihi, ya kuma jaddada kudurinsu na ciyar da rayuwar bil’adama gaba. Ya ce, “Gasar Olympics wata alama ce ta hadin kai, da abokantaka da kuma fahimtar juna. Bari mu dage wajen cimma burin da kasashenmu biyu suka kulla a lokacin kulla huldar diflomasiyya, mu kara dankon zumuncin gargajiya, da aiwatar da taken Olympic na ‘Mu Kara Sauri, da Girma, da Karfi da kuma Yin Hadin Gwiwa’. Mu hada hannu don bude wani sabon zamani na hadin gwiwa tsakanin Sin da Faransa da kuma rubuta sabon babi na gina al’umma mai makoma mai ma’ana ga bil’Adama.” (Mohamed Yahaya)

Labarai Masu Nasaba

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministar Congo Kinshasa: Cibiyar Al’adu Ta Tsakiyar Afirka Ta Kara Shaida Nasarar Hadin Gwiwar Kasar Da Kasar Sin

Next Post

Anya Nahiyar Afirka Fili Ne Na Gudanar Da Takara?

Related

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

17 hours ago
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

18 hours ago
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

19 hours ago
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha
Daga Birnin Sin

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

20 hours ago
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu
Daga Birnin Sin

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

1 day ago
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

1 day ago
Next Post
Anya Nahiyar Afirka Fili Ne Na Gudanar Da Takara?

Anya Nahiyar Afirka Fili Ne Na Gudanar Da Takara?

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

May 10, 2025
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

May 10, 2025
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

May 10, 2025
Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

May 10, 2025
Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

May 10, 2025
Olympics

ECOWAS Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Afrika Ta Yamma – Kwamred Bishir Dauda

May 10, 2025
Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

May 10, 2025
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

May 10, 2025
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

May 10, 2025
Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.