• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gasar Olympics Na Kyautata Abota, Da Inganta Makomar Bai daya

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Gasar Olympics Na Kyautata Abota, Da Inganta Makomar Bai daya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sau da dama mu kan nakalto Pierre de Coubertin, wanda ya kafa kwamitin Olympics na kasa da kasa kuma aka fi sani da uban wasannin Olympics na zamani, inda ya ce, “Shiga gasar wasannin Olympics ya fi lashe gasar muhimmanci, saboda muhimmin abu a rayuwa ba shi ne yin nasara ba, amma yin fafutuka cike da kwarin gwiwa shi ne nasara. Yada wadannan ka’idoji na karfafa gwiwa, da jarumta, da gina bil Adama mai kishi da karimci.” Tabbas wannan batu haka yake, saboda gasar wasannin Olympics ta dade da sauya manufarta ta zakulo mafi kyawun ‘yan wasa a duniya, yanzu ta zama dandalin cudanyar bil’adama, bege da mafarkai, da zaman lafiya da hadin kai. Wasanni gaba daya, musamman wasannin Olympics, na hada kan jama’a ba tare da la’akari da bambancin matsayi na shugabanci, ko siyasa ko addini ba. Kasar Faransa ce ta karbi bakunci gasar Olympics ta bana wadda ta gudana daga ranar 25 ga Yuli zuwa ta 11 ga Agusta. ’Yan wasa sun fafata tsakaninsu cike da kauna da kishin kasashensu a zuciya yayin da suka yi cudanya da takwarorinsa cikin nishadi da annushwa.

 

Bana ce ta cika shekaru 60 da kulla huldar diflomasiya tsakanin Sin da Faransa, kuma gasar wasannin Olympic ta sake ba da damammaki ga kasashen biyu wajen karfafa dankon zumuncin dake tsakaninsu, kuma ta yin hakan, za su sa kaimi ga yin hadin gwiwa bisa la’akari da muhimmancin samun ci gaba a duniya. A kwanakin da suka biyo bayan bikin bude gasar, mun ga sakonni da dama a kafar yanar gizo daga abokai na kasar Sin wadanda suka yaba da gagarumin gudummawa da kasar Sin ta bayar ga nasarar bikin a birnin Paris.

 

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana ruhin Olympics a yayin da ya kai ziyara kasar Faransa a watan Mayun shekarar 2024, domin halartar bikin rufe taro karo na shida na kwamitin ‘yan kasuwa na Sin da Faransa, inda ya ce, yana kallon wasannin Paris a matsayin wata dama ga kasashen biyu wajen zurfafa dangantakarsu ta tarihi, ya kuma jaddada kudurinsu na ciyar da rayuwar bil’adama gaba. Ya ce, “Gasar Olympics wata alama ce ta hadin kai, da abokantaka da kuma fahimtar juna. Bari mu dage wajen cimma burin da kasashenmu biyu suka kulla a lokacin kulla huldar diflomasiyya, mu kara dankon zumuncin gargajiya, da aiwatar da taken Olympic na ‘Mu Kara Sauri, da Girma, da Karfi da kuma Yin Hadin Gwiwa’. Mu hada hannu don bude wani sabon zamani na hadin gwiwa tsakanin Sin da Faransa da kuma rubuta sabon babi na gina al’umma mai makoma mai ma’ana ga bil’Adama.” (Mohamed Yahaya)

Labarai Masu Nasaba

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministar Congo Kinshasa: Cibiyar Al’adu Ta Tsakiyar Afirka Ta Kara Shaida Nasarar Hadin Gwiwar Kasar Da Kasar Sin

Next Post

Anya Nahiyar Afirka Fili Ne Na Gudanar Da Takara?

Related

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

15 hours ago
Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI
Daga Birnin Sin

Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

16 hours ago
A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon
Daga Birnin Sin

A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

17 hours ago
Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

18 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

19 hours ago
Membobin Tawagar Koli Ta Sin Sun Ziyarci Jami’ai Da Gidajen Al’umma A Yankunan Jihar Xinjiang
Daga Birnin Sin

Membobin Tawagar Koli Ta Sin Sun Ziyarci Jami’ai Da Gidajen Al’umma A Yankunan Jihar Xinjiang

20 hours ago
Next Post
Anya Nahiyar Afirka Fili Ne Na Gudanar Da Takara?

Anya Nahiyar Afirka Fili Ne Na Gudanar Da Takara?

LABARAI MASU NASABA

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

September 27, 2025
Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

September 27, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Uba Sani Ya Jagoranci Yunƙurin Ƙara Yawan Rajistar Masu Zaɓe a Jihar Kaduna

September 27, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

September 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

September 27, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

September 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.