• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cututtukan Da Suka Fi Addabar Kajin Gidan Gona Lokacin Damina

by Sulaiman, CGTN Hausa and Abubakar Abba
10 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Cututtukan Da Suka Fi Addabar Kajin Gidan Gona Lokacin Damina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Fannin kiwon Kajin gidan gona, na daya daga cikin fannin da ke saurin fadada, musamman duba da yadda fanin ke samar da ayyukan yi tare da samar wa wadanda suka rungume shi kudaden shiga da kuma rage yawan mazauna karkara da ke kwararowa zuwa cikin birane.

Don haka, ga wasu matakai biyar da mai kiwon Kajin gidan gona zai kaucewa yin asara:
1-Gina masu ingantaccen dakin kwana: Ana bukatar mai kiwon Kajin gidan gona ya tabatar ya gina musu ingantaccen dakin kwana, wanda hakan zai kare su daga kamuwa da sanyi, ana kuma so a rika sauya musu ruwan sha, domin gudun ka da su kamu da wasu cututtuka.
2- Ana so a tabbatar da muhallin da ake kiwonsu ya kansance tsaftace, don kaucewa bullar kwayoyin cutar da za su iya harbin su.
3- Ana so a rika duba yanayin lafiyarsu lokaci bayan lokaci:
Idan ana barin su suna shan ruwan kasa, za su iya harbuwa da kwayoyin cuta, musamman tsutsar ciki da za ta iya yi musu illa, sannan kuma duk irin yawan abincin da suka ci; ba za su yi wani nauyi ba, karshe ma za a ga suna ramewa.
Domin gujewa hakan, yana da kyau a rika duba lafiyarsu akai-akai, ta hanyar bin shawarwarin kwararrun masu kiwo.
4- Ana so a rika sanya musu haske a dakunan kwanansu:
Wannan zai ba su damar yin kwansu a cikin tsakani, musamman duba da cewa; suna da bukatar samun haske har na sa’oi 16, musamman don samun damar yin kwai masu yawan gaske.
5- Ciyar da su wadataccen abinci:
Ana bukatar a rika ciyar da su wadataccen abinci, yadda za su rika samun yawan dumi a jikinsu.
6- Yi musu inshora: Ana so a yi musu inshora don kaucewa yin asara duba da cewa, a lokacin damina sukan fuskanci wasu matsaloli ko cututtuka wadanda ke sa su rage yin kwai kamar yadda suka saba yi da yawa.
Wasu daga cikin cututukan da ke harbin Kajin gidan gona da damina:
a-Kurajen Kaji: Wannan wata babbar cuta ce da ke yi wa Kajin gidan gonar da suka harbu da ita illa. Akasari suna kamuwa da cutar ce, idan Sauro ya cije su da sauran kwarin da suka tsotsi Jinin jikinsu, wanda hakan na kashe su nan take.
Za a iya magance hakan ne, ta hanyar yi musu rigakafin kamuwa da cutar da kuma yi wa wajen kwanansu feshi.
b- Gudawa: Ita ma wannan cuta ce da ke yi wa Kajin gidan gonar da suka kamu da ita illa ga lafiyarsu, wadda har ma tana iya kai su ga halaka ko mutuwa. Akasari, ta fi harbin ‘yan Tsaki masu tsawon mako shida zuwa sama.
Cutar ta fi yaduwa a lokacin damina, idan sun kamu ba sa iya cin abinci; suna kuma yin numfashi ne da kyar da sauran makamantansu.
c- Zawo: Ita ma wannan cutar na harbin Kajin gidan gona daga kowane matakin girma nasu.
d- Cutar sanyi: Idan ana muku-mukun sanyi, suna fuskantar matsala; wanda take kaiwa ga ba sa jin dadin muhallin da ake kiwata su. Za a iya magance musu wannan matsalar kadai ta hanyar yin feshi a inda ake kiwon su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Al’ummar Arewa: Bango Ne Ya Tsage Kadangare Ya Samu Wurin Shiga

Next Post

Gwamnan Kano Ya Naɗa Shugaban Sabuwar Ma’aikatar Tsaro

Related

Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

2 hours ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
Gwamnan Kano Ya Naɗa Shugaban Sabuwar Ma’aikatar Tsaro

Gwamnan Kano Ya Naɗa Shugaban Sabuwar Ma'aikatar Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.