• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Ko Sabon Yunkurin Su Shekarau Zai Kai Arewa Ga Gaci?

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
1 year ago
Shekarau

Wata sabuwar kungiyar fitattun jagororin siyasa daga yankin krewa ta fito, mai suna ‘League of Northern Democrats’ (LND), wadda ta ce za ta gudanar da wani babban taro mai ma’ana don farfado da martabar siyasa da tattalin arzikin yankin arewacin Nijeriya.

 

Kungiyar wadda ta bayyana aniyarta na hada kai tare da mayar da yankin arewa a matsayin sahun gaba a fagen siyasar Nijeriya, ta kuma bayyana cewa gaba daya damuwarta ita ce ci gaban arewacin Nijeriya, inda ta jaddada cewa ba ta gabatar da wani bukatu na kashin kai ga kowa sai ga yankin arewacin Nijeriya.

  • Na Yi Alƙawarin Kawo Wa APC Kano A Zaɓen 2027 – Doguwa
  • Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

Kungiyar mai mutane 226, karkashin jagorancin tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Ibrahim Shekarau, a matsayin shugaban riko da Umar Ardo, a matsayin mai kira da Hon. Emmanuel Jime a matsayin sakataren rikon kwarya da tsofaffin gwamnoni da ‘yan majalisar tarayya da ‘yan kasuwa.

 

LABARAI MASU NASABA

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Bayan Shekarau da Ardo, wasu daga cikin manyan masu fada a ji a kungiyar sun hada da Alhaji Tanko Yakasai, Sanata. Ibrahim Ida, PhD, CON (Wazirin Katsina); Kabir Tafida (Sarki Fadan Sakkwata); Falalu Bello; Dakta Jamilu Isyaka Gwamna (Sardauna Gombe); Emmanuel Jime da kuma Mohammed Kumalia.

 

Sauran sun hada da Malam Salihu Lukman, Amb. Usman Sarki, Injiniya Dallaji Nuhu, Farfesa Usman Yusuf, Muktari Abubakar Tafawa Balewa, Aminu Shehu Shagari, da Murtala Shehu Yar’adua (Tafidan Katsina), da sauransu.

 

Bayan gudanar da wani taro da aka yi a cibiyar ‘Yar’adua da ke Abuja, kungiyar ta yanke shawarar ba da fifiko kan hadin kan siyasar arewacin Nijeriya.

 

“Bayan cimma matsaya a tsakaninmu, mun himmatu wajen inganta al’ummarmu da samar da hadin kai. Wannan hadin kai ne zai zama ginshikin kokarin da muke yi na mayar da arewa a matsayin jagaba a fagen siyasar Nijeriya.”

 

Sun kuma yanke shawarar rubuta wa masu ruwa da tsaki a arewacin Nijeriya don samun goyon bayansu da shiga harkokin kungiyar.

 

A cikin wadanda za a tuntuba sun hada da dukkan tsoffin shugabannin kasa da dukkan tsoffin mataimakan shugaban kasa da masu rike da madafun iko da tsofaffin shugabannin majalisar dattawa da tsofaffin shugabannin majalisar wakilai da tsoffin alkalai da tsoffin hafsoshin soja da sufeto Janar na ’yansanda da Kwanturolan Janar na Kwastam da shugaban hukumar shige da fice da na hukumar jidan yari da manyan-manyan dattawan jihohi da ‘yan kasuwa da manyan ma’aikata da kungiyoyin kwadago da sauran wasu abubuwan da suka dace.

 

A cewar kungiyar, shigar wadannan masu ruwa da tsaki na da matukar muhimmanci wajen samun nasarar ayyukanta.

 

Da yake amsa tambayoyin manema labarai jim kadan bayan taron, Malam Shekarau ya ce kungiyar za ta mayar da hankali ne kan batutuwan da suka shafi ci gaba arewacin Nijeriya ba muradin kowa ba.

 

Ya ce ‘yan kungiyar za su bullo da wasu dabaru na yadda za a inganta al’umma a yankin arewa ta hanyar wayar da kan jama’a kan irin kalubalen da suke fuskanta da bukatunsu na yau da kullum.

 

Ya ce za su wayar da kan al’umma kan bukatar shugabanci na gari, bunkasar tattalin arziki da samun dukiya da dacewa da ilimi da tsaro da hadin kai.

 

Ya kara da cewa, “Tunani ne na siyasa, ba wai game da wani mutum ko jam’iyya ba, kuma yana da matukar muhimmanci game da zaben 2027. Wannan batun da ya dauki shekaru mai yawa. Muna son samar da kundi wanda ya zarce shekara guda, shekara biyu, ko shekara 10.”

 

A nasa bangaren, Umar Ardo ya ce, “Mutanen arewa za su hada kai wuri guda domin magance matsalolin yanki arewa. Ba mu damu da matsalar nada mukamai ba, mun damu da matsalolin rashin tsaro, yunwa, talauci da na tattalin arziki da ke addabar arewa.

 

“Ba mu damu da batun nade-naden ba, domin yana zuwa ne wuce, amma muhimmin batu shi ne a warware wadannan matsaloli da suke damun arewa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
Manyan Labarai

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025
Next Post
Firaministan Fiji: Akwai Abubuwa Da Dama Da Kasarmu Za Ta Koyo Daga Wajen Sin

Firaministan Fiji: Akwai Abubuwa Da Dama Da Kasarmu Za Ta Koyo Daga Wajen Sin

LABARAI MASU NASABA

Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025
Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

October 31, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida

October 31, 2025
Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.