• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abokin Da Ke Iya Ba Ka Taimako A Lokacin Da Kake Bukata, Shi Ne Aboki Na Kwarai

byCGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Aboki

Akwai nisan kimanin kilomita dubu 10 tsakanin Kenya da kasar Sin, to, amma ko kun san tsawon lokacin da aka dauka wajen jigilar wani furen rose da aka tsinta daga gonar da ke kasar ta Kenya zuwa kasar Sin?

 

Allah ya hore wa kasar Kenya albarkatun furanni irinsu Rose, har ma kasar ta kasance kasar da ta fi yawan fitar da furanni zuwa ketare a nahiyar Afirka. Sai dai a baya, a kan shafe tsawon kwanaki uku kafin a kai furannin kasar Kenya kasuwannin kasar Sin, lokacin da ya yi matukar raguwa zuwa sa’o’i 17 kawai a yanzu.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
  • Inganta Raya Shawarar BRI Zai Zama Daya Daga Manyan Batutuwan Da Za A Tattauna A Gun Taron Kolin FOCAC Na Bana

Amma me ya haifar da wannan babban sauyi mai ban mamaki? Amsa ita ce matakan da kasar Sin ta yi ta dauka na inganta hadin gwiwarta da kasashen Afirka ta fannin cinikayya. Idan ba mu manta ba, a watan Nuwamban shekarar 2021, gwamnatin kasar Sin ta sanar da samar da matakai masu sauki kan amfanin gona da ke shigowa daga kasashen Afirka, inda ta rage tsawon lokaci na binciken cututtuka da ma fadada kayayyakin da ake cire musu harajin kwastam da sauransu, matakan da suka fadada hanyoyi zuwa kasuwannin kasar Sin ga amfanin gonar kasashen Afirka, ciki har da furannin kasar Kenya da Avokado da lemo da Abarba da sauransu. Ya zuwa watan Yunin bara, akwai nau’o’in amfanin gona 16 na kasashen Afirka 11 da kasar Sin ta shigo da su kasuwanninta sakamakon matakan, an kuma cire harajin kwastam a kan kaso 98% na kayayyakin da kasar Sin ta shigo daga wasu kasashen Afirka 21.

 

LABARAI MASU NASABA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

Ban da haka, kasar Sin ta kuma kafa bikin baje kolin kayayyakin da take shigowa da su kasa da kasa, da bikin baje kolin tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Afirka da musamman ta kafa domin kasashen Afirka, da sauransu, don yayata kayayyakin kasashen Afirka a kasuwanninta.

 

Cinikin waje na daya daga cikin manyan gishikai uku da ke samar da bunkasar tattalin arziki, don haka ma kullum ake saka batun bunkasa ciniki a matsayin daya daga cikin muhimman fannoni na hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka. Bisa ingantattun matakan da aka ta dauka a gun tarurukan dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da kasashen Afirka ya yi ta bunkasa tare da haifar gaggaruman nasarori, inda a cikin shekaru 15 a jere, kasar Sin ta kasance abokin cinikayya mafi girma ga nahiyar Afirka, a bara kuma, jimillar ciniki a tsakanin sassan biyu har ta kai wani matsayin tarihi na dala biliyan 282.1.

 

Sakamakon makamancin abin da ya faru gare su a tarihi da ma buri daya da suke neman cimmawa, kasar Sin ta san mene ne aminanta na Afirka ke fatan cimmawa, don haka ma take son raba damammaki da su don tabbatar da hadin gwiwar cin moriyar juna.

 

Kamar yadda bature kan ce, abokin da ke iya ba ka taimako a lokacin da kake bukata, shi ne aboki na kwarai. Abin haka yake, wanda kuma hakan ya shaida huldar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka.(Mai zane:Mustapha Bulama)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka
Ra'ayi Riga

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

September 30, 2025
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

September 29, 2025
Next Post
Muhalli Mai Kyau Na Kasar Sin Ya Sake Dawo Da Giwaye

Muhalli Mai Kyau Na Kasar Sin Ya Sake Dawo Da Giwaye

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version