ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abokin Da Ke Iya Ba Ka Taimako A Lokacin Da Kake Bukata, Shi Ne Aboki Na Kwarai

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Aboki

Akwai nisan kimanin kilomita dubu 10 tsakanin Kenya da kasar Sin, to, amma ko kun san tsawon lokacin da aka dauka wajen jigilar wani furen rose da aka tsinta daga gonar da ke kasar ta Kenya zuwa kasar Sin?

 

Allah ya hore wa kasar Kenya albarkatun furanni irinsu Rose, har ma kasar ta kasance kasar da ta fi yawan fitar da furanni zuwa ketare a nahiyar Afirka. Sai dai a baya, a kan shafe tsawon kwanaki uku kafin a kai furannin kasar Kenya kasuwannin kasar Sin, lokacin da ya yi matukar raguwa zuwa sa’o’i 17 kawai a yanzu.

ADVERTISEMENT
  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
  • Inganta Raya Shawarar BRI Zai Zama Daya Daga Manyan Batutuwan Da Za A Tattauna A Gun Taron Kolin FOCAC Na Bana

Amma me ya haifar da wannan babban sauyi mai ban mamaki? Amsa ita ce matakan da kasar Sin ta yi ta dauka na inganta hadin gwiwarta da kasashen Afirka ta fannin cinikayya. Idan ba mu manta ba, a watan Nuwamban shekarar 2021, gwamnatin kasar Sin ta sanar da samar da matakai masu sauki kan amfanin gona da ke shigowa daga kasashen Afirka, inda ta rage tsawon lokaci na binciken cututtuka da ma fadada kayayyakin da ake cire musu harajin kwastam da sauransu, matakan da suka fadada hanyoyi zuwa kasuwannin kasar Sin ga amfanin gonar kasashen Afirka, ciki har da furannin kasar Kenya da Avokado da lemo da Abarba da sauransu. Ya zuwa watan Yunin bara, akwai nau’o’in amfanin gona 16 na kasashen Afirka 11 da kasar Sin ta shigo da su kasuwanninta sakamakon matakan, an kuma cire harajin kwastam a kan kaso 98% na kayayyakin da kasar Sin ta shigo daga wasu kasashen Afirka 21.

 

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Ban da haka, kasar Sin ta kuma kafa bikin baje kolin kayayyakin da take shigowa da su kasa da kasa, da bikin baje kolin tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Afirka da musamman ta kafa domin kasashen Afirka, da sauransu, don yayata kayayyakin kasashen Afirka a kasuwanninta.

 

Cinikin waje na daya daga cikin manyan gishikai uku da ke samar da bunkasar tattalin arziki, don haka ma kullum ake saka batun bunkasa ciniki a matsayin daya daga cikin muhimman fannoni na hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka. Bisa ingantattun matakan da aka ta dauka a gun tarurukan dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da kasashen Afirka ya yi ta bunkasa tare da haifar gaggaruman nasarori, inda a cikin shekaru 15 a jere, kasar Sin ta kasance abokin cinikayya mafi girma ga nahiyar Afirka, a bara kuma, jimillar ciniki a tsakanin sassan biyu har ta kai wani matsayin tarihi na dala biliyan 282.1.

 

Sakamakon makamancin abin da ya faru gare su a tarihi da ma buri daya da suke neman cimmawa, kasar Sin ta san mene ne aminanta na Afirka ke fatan cimmawa, don haka ma take son raba damammaki da su don tabbatar da hadin gwiwar cin moriyar juna.

 

Kamar yadda bature kan ce, abokin da ke iya ba ka taimako a lokacin da kake bukata, shi ne aboki na kwarai. Abin haka yake, wanda kuma hakan ya shaida huldar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka.(Mai zane:Mustapha Bulama)

 

Aboki
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Aboki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Muhalli Mai Kyau Na Kasar Sin Ya Sake Dawo Da Giwaye

Muhalli Mai Kyau Na Kasar Sin Ya Sake Dawo Da Giwaye

LABARAI MASU NASABA

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.