• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sabon Tsarin Kofin Zakarun Turai Zai Kasance

by Abba Ibrahim Wada
9 months ago
in Wasanni
0
Yadda Sabon Tsarin Kofin Zakarun Turai Zai Kasance
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid mai rike da kofin gasar zakarun Turai ta Champions za ta fafata da Liberpool a zagayen farko na gasar da aka sauya wa fasali ta 2024-25 a sabon tsarin da hukumar ta nahiyar turai ta fitar.

A satin da ya gabata ne aka raba jadawalin sabon tsarin gasar da za a fara amfani da shi a kakar wasa ta bana mai kungiyoyi 36 kuma sauran kungiyoyin da Real Madrid za ta fafata da su a zagayen su ne Dortmund, AC Milan, Atalanta, Salzburg, Lille, Stuttgart, Brest.

  • Mutum Miliyan 7.9 Da Ta’addanci Ya Tagayyara A Jihohi 3 Na Bukatar Agaji – UNOCHA
  • Champions League: Real Madrid Ta Zama Zakara Bayan Doke Dortmund

Muhimmin sauyi da kwamitin zartarwa na UEFA ya sanar shi ne ficewa daga tsarin matakin rukuni da ake yi a baya, inda a yanzu kowace kungiya za ta buga wasa takwas – hudu a gida, hudu a waje, amma ba gida da waje ba.

A baya matakin rukuni na gasar zakarun Turai ya kunshi kungiyoyi 32, da ake rabawa cikin rukuni takwas, inda kowanne rukuni ke kunshe da kungiyoyi hudu, sannan sauran wasannin da za su fi zafi a zageyn sun hada da wanda PSG za ta kara da kungiyoyin Manchester City, Bayern Munich, Atletico Madrid, Arsenal.

Yadda jadawalin sabon tsarin zai kasance

Labarai Masu Nasaba

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

A yanzu kungiyoyi 36 ne za su shiga gasar, mai tsarin lig daya, inda duka kungiyoyin za su kasance a teburi daya domin tantance kungiyoyin da za su fafata da juna, da farko an rarraba su a cikin tukwane hudu bisa matsayin kowace kungiya.

An yi amfani da wata manhaja da UEFA ta samar domin fitar da kungiyoyin da kowacce kungiya za ta fafata da su kuma a matakin farko babu kungiyar da za ta fafata da abokiyar hamayyarta da suka fito daga kasa daya. Hakan na nufin kowace kungiya za ta kara da kungiyoyi biyu daga kowace tukunya cikin hudu.

Wasannin Man City

Bayern Munich (a gida) Borussia Dortmund (a waje) Atalanta ( a gida) Benfica (a waje) Young Boys (a gida) Red Star Belgrade (a waje) Brest (h) Monaco (a)

Wasannin Arsenal

PSG (a gida) Inter Milan (a waje) Shakhtar Donestsk (a gida) Atalanta (a waje) Dinamo Zagreb (a gida) Sporting CP (a waje) Monaco (a gida) Girona (a waje)

Wasannin Bercelona

Bayern Munich (a gida) Borussia Dortmund (a waje) Atalanta (a gida) Benfica (a waje)

Young Boys (a gida) Red Star Belgrade (a waje) Brest (a gida) Monaco (a waje)

Sannan idan aka kammala wasannin zagayen farko kungiyoyin za su kasance a teburi daya wato daga na daya zuwa na 36 inda daga nan ne kuma sai kungiyoyi takwas na saman teburi su tsallaka kai-tsaye zuwa zagayen ‘yan 16, yayin da daga kan kungiya ta tara zuwa 24 za su yi wasan neman gurbi (gida da waje), don kaiwa zagayen ‘yan 16.

Su kuwa wadanda suka kare a matsayi na 25 zuwa 36, an fitar da su daga gasar kenan, kuma ba za su samu damar shiga gasar Europa League ba, kamar yadda ake yi a baya hakan yana nufin an daina tafiya gasar Europa daga kofin zakarun Turai.

Daga kan matakin zagayen ‘yan 16 kuma sai a ci gaba da yadda aka saba gudanar da ita a baya – wato a kai matakin dab da kusa da na karshe, da matakin kusa da karshe, har zuwa wasan karshe, wanda za a yi a Birnin Munich na kasar Jamus, sannan yawan wasannin da za a fafata a sabon tsarin zai karu daga 125 zuwa 189.

Kowace kungiya za ta yi wasa takwas mafi karanci maimakon shida da kungiyoyin da ake fitarwa daga gasar tun a rukuni ke samun damar yi a baya, sannan za a gudanar da wasan zagayen farko har zuwa karshen watan Janairu, maimakon a baya da yake karewa kafin bikin Kirsimeti.

Wadanne kungiyoyi ne za su buga gasar a bana?

Tukunyar farko: Real Madrid (Spa), Man City (Eng), Bayern Munich (Ger), Paris St-Germain (Fra), Liberpool (Eng), Inter Milan (Ita), Dortmund (Ger), Leipzig (Ger), Barcelona (Spa) Tukunya ta biyu: Bayer Leberkusen (Ger), Atletico Madrid (Spa), Atalanta (Ita), Jubentus (Ita), Benfica (Por), Arsenal (Eng), Club Brugge (Bel),

Shakhtar Donetsk (Ukr), AC Milan (Ita).

Tukunya ta uku: Feyenoord (Ned), Sporting Lisbon (Por), PSB Eindhoben (Ned), Dinamo Zagreb (Cro), Salzburg (Aus), Lille (Fra), Red Star

Belgrade (Ser), Young Boys (Sui), Celtic (Sco).

Tukunya ta hudu: Sloban Bratislaba (Ska), Monaco (Fra), Sparta Prague (Cze), Aston Billa (Eng), Bologna (Ita), Girona (Spa), Stuttgart (Ger), Sturm Graz (Aus), Brest (Fra)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ChampionFIFAFOOTBALL
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Ware Kudi Domin Tallafawa Yankunan Da Ambaliya Da Guguwa Suka Aukawa

Next Post

Afrika Ta Kudu Na Neman Hadin Gwiwa Da Sin Wajen Zamanantar Da Kanta

Related

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu
Wasanni

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

19 minutes ago
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan
Wasanni

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

3 hours ago
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal
Wasanni

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

3 hours ago
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona
Wasanni

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

2 days ago
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Wasanni

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

4 days ago
Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

5 days ago
Next Post
Afrika Ta Kudu Na Neman Hadin Gwiwa Da Sin Wajen Zamanantar Da Kanta

Afrika Ta Kudu Na Neman Hadin Gwiwa Da Sin Wajen Zamanantar Da Kanta

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.