• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sabon Tsarin Kofin Zakarun Turai Zai Kasance

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
Turai

Kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid mai rike da kofin gasar zakarun Turai ta Champions za ta fafata da Liberpool a zagayen farko na gasar da aka sauya wa fasali ta 2024-25 a sabon tsarin da hukumar ta nahiyar turai ta fitar.

A satin da ya gabata ne aka raba jadawalin sabon tsarin gasar da za a fara amfani da shi a kakar wasa ta bana mai kungiyoyi 36 kuma sauran kungiyoyin da Real Madrid za ta fafata da su a zagayen su ne Dortmund, AC Milan, Atalanta, Salzburg, Lille, Stuttgart, Brest.

  • Mutum Miliyan 7.9 Da Ta’addanci Ya Tagayyara A Jihohi 3 Na Bukatar Agaji – UNOCHA
  • Champions League: Real Madrid Ta Zama Zakara Bayan Doke Dortmund

Muhimmin sauyi da kwamitin zartarwa na UEFA ya sanar shi ne ficewa daga tsarin matakin rukuni da ake yi a baya, inda a yanzu kowace kungiya za ta buga wasa takwas – hudu a gida, hudu a waje, amma ba gida da waje ba.

A baya matakin rukuni na gasar zakarun Turai ya kunshi kungiyoyi 32, da ake rabawa cikin rukuni takwas, inda kowanne rukuni ke kunshe da kungiyoyi hudu, sannan sauran wasannin da za su fi zafi a zageyn sun hada da wanda PSG za ta kara da kungiyoyin Manchester City, Bayern Munich, Atletico Madrid, Arsenal.

Yadda jadawalin sabon tsarin zai kasance

LABARAI MASU NASABA

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

A yanzu kungiyoyi 36 ne za su shiga gasar, mai tsarin lig daya, inda duka kungiyoyin za su kasance a teburi daya domin tantance kungiyoyin da za su fafata da juna, da farko an rarraba su a cikin tukwane hudu bisa matsayin kowace kungiya.

An yi amfani da wata manhaja da UEFA ta samar domin fitar da kungiyoyin da kowacce kungiya za ta fafata da su kuma a matakin farko babu kungiyar da za ta fafata da abokiyar hamayyarta da suka fito daga kasa daya. Hakan na nufin kowace kungiya za ta kara da kungiyoyi biyu daga kowace tukunya cikin hudu.

Wasannin Man City

Bayern Munich (a gida) Borussia Dortmund (a waje) Atalanta ( a gida) Benfica (a waje) Young Boys (a gida) Red Star Belgrade (a waje) Brest (h) Monaco (a)

Wasannin Arsenal

PSG (a gida) Inter Milan (a waje) Shakhtar Donestsk (a gida) Atalanta (a waje) Dinamo Zagreb (a gida) Sporting CP (a waje) Monaco (a gida) Girona (a waje)

Wasannin Bercelona

Bayern Munich (a gida) Borussia Dortmund (a waje) Atalanta (a gida) Benfica (a waje)

Young Boys (a gida) Red Star Belgrade (a waje) Brest (a gida) Monaco (a waje)

Sannan idan aka kammala wasannin zagayen farko kungiyoyin za su kasance a teburi daya wato daga na daya zuwa na 36 inda daga nan ne kuma sai kungiyoyi takwas na saman teburi su tsallaka kai-tsaye zuwa zagayen ‘yan 16, yayin da daga kan kungiya ta tara zuwa 24 za su yi wasan neman gurbi (gida da waje), don kaiwa zagayen ‘yan 16.

Su kuwa wadanda suka kare a matsayi na 25 zuwa 36, an fitar da su daga gasar kenan, kuma ba za su samu damar shiga gasar Europa League ba, kamar yadda ake yi a baya hakan yana nufin an daina tafiya gasar Europa daga kofin zakarun Turai.

Daga kan matakin zagayen ‘yan 16 kuma sai a ci gaba da yadda aka saba gudanar da ita a baya – wato a kai matakin dab da kusa da na karshe, da matakin kusa da karshe, har zuwa wasan karshe, wanda za a yi a Birnin Munich na kasar Jamus, sannan yawan wasannin da za a fafata a sabon tsarin zai karu daga 125 zuwa 189.

Kowace kungiya za ta yi wasa takwas mafi karanci maimakon shida da kungiyoyin da ake fitarwa daga gasar tun a rukuni ke samun damar yi a baya, sannan za a gudanar da wasan zagayen farko har zuwa karshen watan Janairu, maimakon a baya da yake karewa kafin bikin Kirsimeti.

Wadanne kungiyoyi ne za su buga gasar a bana?

Tukunyar farko: Real Madrid (Spa), Man City (Eng), Bayern Munich (Ger), Paris St-Germain (Fra), Liberpool (Eng), Inter Milan (Ita), Dortmund (Ger), Leipzig (Ger), Barcelona (Spa) Tukunya ta biyu: Bayer Leberkusen (Ger), Atletico Madrid (Spa), Atalanta (Ita), Jubentus (Ita), Benfica (Por), Arsenal (Eng), Club Brugge (Bel),

Shakhtar Donetsk (Ukr), AC Milan (Ita).

Tukunya ta uku: Feyenoord (Ned), Sporting Lisbon (Por), PSB Eindhoben (Ned), Dinamo Zagreb (Cro), Salzburg (Aus), Lille (Fra), Red Star

Belgrade (Ser), Young Boys (Sui), Celtic (Sco).

Tukunya ta hudu: Sloban Bratislaba (Ska), Monaco (Fra), Sparta Prague (Cze), Aston Billa (Eng), Bologna (Ita), Girona (Spa), Stuttgart (Ger), Sturm Graz (Aus), Brest (Fra)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana
Wasanni

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars
Wasanni

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta
Labarai

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025
Next Post
Afrika Ta Kudu Na Neman Hadin Gwiwa Da Sin Wajen Zamanantar Da Kanta

Afrika Ta Kudu Na Neman Hadin Gwiwa Da Sin Wajen Zamanantar Da Kanta

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

October 25, 2025
Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi

October 25, 2025
Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025 Gbenga Olu Komolafe

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

October 25, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.