• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Haddasa Cacar Baki Tsakanin Kwankwaso Da PDP?

by Yusuf Shuaibu
12 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Me Ya Haddasa Cacar Baki Tsakanin Kwankwaso Da PDP?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cacar baki ta kaure a tsakanin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Rabiu Musa Kwankwaso da jam’iyyar PDP.

Zazzafar mahawarar dai ta fara ne tun lokacin da Kwankwaso ya bayyana cewa jam’iyyar PDP ta mutu a siyasance.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Kotu Ta Bada Belin Masu Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa Kan Naira Milyan 10 Kowanensu

Da yake magana a ranar Asabar a yayin bude wani ofishin jam’iyyar NNPP da aka yi wa gyara a Jihar Katsina, Kwankwaso ya ce shi da mabiyansa sun bar PDP ne saboda ta mutu.

“Ina so in tunatar da ku cewa PDP ta mutu saboda mun bar jam’iyyar. Tun da sun fita daga layi sai muka yanke shawarar ficewa,” in ji shi.

Kwankwaso ya kuma ce shi ne zai lashe zaben shugaban kasa a 2027, inda ya ce jam’iyyar NNPP a shirye take ta karbi ragamar shugabancin kasar da sauran jihohi.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Tsohon gwamnan Jihar Kano ya ce bai kamata a yaudari ‘yan Nijeriya da kyauta ko kudi ba a lokacin zabe mai zuwa.

Da take mayar da martini, jam’iyyar PDP ta bayyana cewa Kwankwaso bai da alkibla a siyasar Nijeriya, wanda hakan ta sa ya gaza ya kuma rasa kimansa.

Jam’iyyar PDP ta mayar da martanin ne a cikin wata sanarwa ta hannun sakataren yada labaranta na kasa, Debo Ologunagba, ta soki Kwankwaso da nuna son kai da son zuciya wanda ke nuni da cewa shi ba shugaba ne nagari ba.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Martanin da muka mayar dangane da kalaman da Sanata Rabi’u Kwankwaso shi ne, ba shi da wani tasiri a siyasar Nijeriya a yau idan aka yi la’akari da yadda yake fafutukar shugabancin jam’iyyar mai suna NNPP wadda ita ma ke fafutukar ganin ta mallaki jiha daya kawai.

“Abun takaicin ne a cewa dan siyasar da ya gaza kuma mara tasiri da ke da jiha daya zai yi ikirarin cewa jam’iyyar da ke da gwamnoni 13, da sanatoci da dama da ‘yan majalisar wakilai masu yawa da a dukkan rassan kasar nan.

“Abin da ya fi tayar da hankali shi ne, yadda Sanata Kwankwaso ya nuna tsananin son kai da son zuciya, wanda hakan ke nuna cewa shi ba shugaba ba ne.”

Jam’iyyar PDP ta bayyana Kwankwaso a matsayin dan siyasar mara alkibla da wanda ya samu nasarorinsa ta hanyar tsarin jam’iyyar PDP.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Abin takaici ne a wannan lokaci da jam’iyyar PDP da ‘yan Nijeriya masu kishin kasa ke tofa albarkacin bakinsu dangane da tsananin wahalhalun da kasar nan ke fuskanta sakamakon manufofin gwamnatin APC na kin jinin jama’a, a wannan lokacin ‘yan Nijeriya ciki har da gidan Sanata Kwankwaso na Jihar Kano na fama da yunwa.

“A daidai lokacin da ‘yan Nijeriya sama da miliyan 150 suka tsunduma cikin bakin talauci, a kullum miliyoyin ‘yan Nijeriya ke asarar hanyoyin samun abinci a lokacin da darajar naira ta fadi zuwa fiye da naira 1,600 kan dala daya, sannan an samu kashi 34 na hauhawar farashin man fetur wanda ya kai lita daya naira 1,200 a sannan kasar nan sakamakon munannan manufofin APC. Burin Sanata Kwankwaso shi ne son zama shugaban kasa ba tare da nuna damuwa kan halin da kasar nan ke ciki ba. Wannan babban abin takaici ne matuka.

“Don haka jam’iyyar PDP ba za ta tsaya cacar baki da shi ba kan irin wannan nuna son kai da rashin sanin ya kamata. Ko ta wace fuska, duk nasarar da Kwankwaso ya samu a siyasance, ya samu ne ta sanadiyyar PDP.”

Wannan dambarwa dai ta sake jefa shakku a kan yiwuwar kawancen da ake tunanin zai iya kulluwa a tsakanin Atiku da Kwankwaso da kuma Obi domin yi wa Shugaban Kasa Tinubu taron dangi a shekarar 2027.

Kana tambayar da ake dakon amsarta har yanzu ita ce, me ya haddasa wannan cacar bakin a tsakanin Kwankwaso da PDP?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kanoKwankwasoPDPSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Muna Fatan Sterling Ya Bai Wa Mara Ɗa Kunya A Arsenal – Arteta

Next Post

Sin Na Shirin Soke Daukacin Haraji Kan Hajojin Dake Shiga Kasar Daga Kasashe Mafiya Karancin Wadata

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

4 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

2 weeks ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Sin Na Shirin Soke Daukacin Haraji Kan Hajojin Dake Shiga Kasar Daga Kasashe Mafiya Karancin Wadata

Sin Na Shirin Soke Daukacin Haraji Kan Hajojin Dake Shiga Kasar Daga Kasashe Mafiya Karancin Wadata

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.