• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gasar Nakasassu Ta Duniya: Yadda Nijeriya Ta Kare A Mataki Na 40

by Abba Ibrahim Wada
9 months ago
in Wasanni
0
Gasar Nakasassu Ta Duniya: Yadda Nijeriya Ta Kare A Mataki Na 40
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Lahadin satin da ya gabata ne aka kammala wasannin Nakasassu da ya hada ‘yan wasa daga sassa daban-daban na Duniya kamar yadda aka kammala na masu lafiya a watan da ya gabata a kasar ta Faransa.

Sai dai daman tun farko hukumomin Birnin na Paris sun yi alkawarin gudanar da gasar da za a dade ana tuna ta yayin da suke shirin karbar bakuncin gasar Olympics ta Nakasassu ta wannan shekara ta 2024.

  • Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku
  • Lallai Ƴan Nijeriya Suke Bibiyar Aiyukan Ƴan Majalisu – Shugaban EFCC

Bayan da aka yi gasar wasannin Tokyo a 2021 ba tare da ‘yan kallo ba saboda Annobar Korona, sannan ita kuma gasar Rio ta 2016 ta gamu da matsalollin kudi , Birnin Paris ya kasance cikin matsin lamba kan ya gudanar da gasar da za ta kasance daidai da wadda aka yi a Birnin Landan a 2012 ko ma gasar ta Paris ta zarta ta.

Bikin bude gasar da za a ranar Larabar da ta gabata da karfe 7:00 na yamma agogon

Nijeriya zai kasance ne a ‘Place de la Concorde’, inda za a bayar da kyaututtuka na lambobin Zinare 549 ga ‘yan wasan da suka yi bajinta a washegari.

Labarai Masu Nasaba

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Sannan an kammala gasar inda aka yi bikin rufewa a filin wasa na Stade de France ranr Lahadi 8 ga watan Satumba 2024, sannan an sayar da tikiti kusan miliyn biyu na shiga gasar zuwa yanzu, inda kuma har yanzu akwai 500,000 da ba a saya ba. Bayan irin nasarar da aka samu ta gasar Olympics da aka kammala a Paris hukumomin birnin sun ce wannan somin-tabi ne.

Gasar ta Paris ta samu ‘yan wasa mata da tawagogin ‘yan wasa da ba a taba samu ba a wata gasa ta Nakasassu ta Olympics, sannan kuma za a nuna a tashoshin talabijin a yankuna da dama masu yawan da ba a taba yi ba a baya.

Kuma Faransa ba ta taba karbar bakuncin wasannin Nakasassu na bazara ba, koda yake ta karbi bakuncin wasannin lokacin hunturu na 1992 da aka yi a Albertbille.

Nijeriya ta kammala wasannin wannan shekarar inda ta kammala a mataki na 40 bayan ta lashe lambar yabo guda bakwai ciki kuwa akwai gwal guda biyu da tagulla guda uku da kuma azurfa guda biyu da aka samu a gasar.

‘Yan wasa irin su Onyinyechi Mark da Folashade Oluwafemiayo da Bose Omolayo da Flora Ugwunwa da Esther Nworgu da sau Ogunkunle su ne suka lashewa Nijeriya wadannan kyaututtukan a wannan shekarar da aka kammala.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GasaNakasassuNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wadanne Jarumai Ne Suka Samu Kyautukan Motoci?

Next Post

Gasar Firimiya: Arsenal Na Cikin Tsaka Mai Wuya

Related

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona
Wasanni

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

1 day ago
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Wasanni

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

3 days ago
Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

5 days ago
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa
Wasanni

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

6 days ago
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano
Labarai

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

7 days ago
Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica
Wasanni

Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

7 days ago
Next Post
Gasar Firimiya: Arsenal Na Cikin Tsaka Mai Wuya

Gasar Firimiya: Arsenal Na Cikin Tsaka Mai Wuya

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.