• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jan Kafar Tinubu Na Cire Harajin Shigo Da Abinci Na Ci Gaba Da Ta’azzara rayuwa

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
11 months ago
in Labarai
0
abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya a karkashin Shugaba Bola Ahmed ta ci gaba da jan kafa wajen aiwatar da afuwar harajin shigo da wasu zababbun kayayyakin abinci tun watannin baya da ta sanar da cewa za ta yi hakan.

Kayan abincin da ya kamata a ce an samu damar shigo da su ba tare wani haraji ko haramcin shigo da su ba, sun hada da shinkafa, dawa, masara, alkama, wake, hatsi, gero na tsawon kwanaki 150 daga ranar 15 ga watan Yuli zuwa 31 ga watan Disamban 2024.

  • Jerin Kasurguman ‘Yan Bindiga Da Sojoji Suka Hallaka A Arewa 
  • Jarumai A Masana’antar Kannywood Sun Jajanta Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

Ministan kudi, Wale Edun shi ne ya sanar da janye harajin shigo da kayan abincin da dage takunkumin shigo da su a watan Yuni a wani yunkurin gwamnati Tinubu na kawo saukin kayan abinci da rage matsin rayuwa da ake fuskanta.

A watan Yuli na 2024, Kwanturola Janar na Hukumar Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi, ya tabbatar da aniyar gwamnati na aiwatar da umarnin janye takunkumin shigo da kayan abincin.

Rahotonni sun ce duk da rahotan hukumar kididdiga (NBS) na watan Yuli da Agusta da suka nuna cewa hauhawar farashin ya kasance daga kaso 39.53 da kaso 37.52 cikin 100, tsadar kayan abinci a kasuwanni na nan a kan tsadarsa sai ma abun da ya karu.

Labarai Masu Nasaba

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

A wani ziyarar kasuwanni da aka gudanar a ranar Litinin, ya nuna cewa buhun shinkafar mai nauyin kilogram 50 ya kan kasance daga naira 87,000 zuwa naira 106,000. Buhun wake 50kg kuwa ana sayar da shi ne kan naira 65,000 zuwa naira 100,000. ‘Yan Nijeriya da dama ba su iya samun damar cin abinci sau uku a rana, inda suka rage yawan cin abinci sakamakon tsadar rayuwa duk kuwa da cewa an janye harajin shigo da wasu kayan abinci.

Da yake magana kan wannan lamarin a ranar Litinin, babban daraktan cibiyar inganta harkokin ‘yan kasuwa masu zaman kansu (CPPE), Muda Yusuf, ya ce, babban matsalar da ke janyo tsadar kayan abincin shi ne, jan kafar aiwatar da cire harajin shigo da kayan abincin.

A cewarsa, akwai babbar matsala tsakanin sanar da wani shiri da aiwatar da shiri a wannan gwamnati, wanda kuma bai kamata ake samun irin wannan matsalar ba.

Ya tabbatar da cewa daga kafa ga shigo da kayayyakin abincin bai samu aiwatarwa yadda ya dace ba, don haka ne ake samun karin matsala ga tattalin arziki na kasar.

Yusuf ya bukaci gwamnati ta tashi tsaye ta aiwatar da wannan shirin nata domin a samu saukin matsin rayuwa da tsadar kayayyakin abinci da jama’a ke fuskanta a halin yanzun.

Shi ma nasa bangaren, Olufemi Kayode, mamba a kungiyar samar da lasisi na kwastam a Nijeriya (ANLCA), ya ce, har yanzu babu cikakken tsarin janye harajin shigo da kayayyakin.

Ya nuna cewa akwai matsala a tsakanin tsarin sanarwar janyewar da kuma manufar aiwatar da shirin daga wajen kwastam. Don haka ne ya nuna cewa akwai bukatar daga ma’aikatar kudi da kwastam da su samar da manufa ta yadda za a aiwatar da janye harajin domin shigo da kayayyakin ba tare da wani kalubale ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamshin Jiki Da Cikar Hankalin Manzon Allah (SAW)

Next Post

Nijeriya Na Bukatar Kujeran Dindindin A Kwamitin Tsaro Na MDD – Ministan Tsaro

Related

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

6 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

9 hours ago
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo
Labarai

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

12 hours ago
Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet
Labarai

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

15 hours ago
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka
Manyan Labarai

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

16 hours ago
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 
Manyan Labarai

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

20 hours ago
Next Post
Ministan Tsaro

Nijeriya Na Bukatar Kujeran Dindindin A Kwamitin Tsaro Na MDD – Ministan Tsaro

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.