• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jan Kafar Tinubu Na Cire Harajin Shigo Da Abinci Na Ci Gaba Da Ta’azzara rayuwa

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
9 months ago
in Labarai
0
abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya a karkashin Shugaba Bola Ahmed ta ci gaba da jan kafa wajen aiwatar da afuwar harajin shigo da wasu zababbun kayayyakin abinci tun watannin baya da ta sanar da cewa za ta yi hakan.

Kayan abincin da ya kamata a ce an samu damar shigo da su ba tare wani haraji ko haramcin shigo da su ba, sun hada da shinkafa, dawa, masara, alkama, wake, hatsi, gero na tsawon kwanaki 150 daga ranar 15 ga watan Yuli zuwa 31 ga watan Disamban 2024.

  • Jerin Kasurguman ‘Yan Bindiga Da Sojoji Suka Hallaka A Arewa 
  • Jarumai A Masana’antar Kannywood Sun Jajanta Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

Ministan kudi, Wale Edun shi ne ya sanar da janye harajin shigo da kayan abincin da dage takunkumin shigo da su a watan Yuni a wani yunkurin gwamnati Tinubu na kawo saukin kayan abinci da rage matsin rayuwa da ake fuskanta.

A watan Yuli na 2024, Kwanturola Janar na Hukumar Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi, ya tabbatar da aniyar gwamnati na aiwatar da umarnin janye takunkumin shigo da kayan abincin.

Rahotonni sun ce duk da rahotan hukumar kididdiga (NBS) na watan Yuli da Agusta da suka nuna cewa hauhawar farashin ya kasance daga kaso 39.53 da kaso 37.52 cikin 100, tsadar kayan abinci a kasuwanni na nan a kan tsadarsa sai ma abun da ya karu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

A wani ziyarar kasuwanni da aka gudanar a ranar Litinin, ya nuna cewa buhun shinkafar mai nauyin kilogram 50 ya kan kasance daga naira 87,000 zuwa naira 106,000. Buhun wake 50kg kuwa ana sayar da shi ne kan naira 65,000 zuwa naira 100,000. ‘Yan Nijeriya da dama ba su iya samun damar cin abinci sau uku a rana, inda suka rage yawan cin abinci sakamakon tsadar rayuwa duk kuwa da cewa an janye harajin shigo da wasu kayan abinci.

Da yake magana kan wannan lamarin a ranar Litinin, babban daraktan cibiyar inganta harkokin ‘yan kasuwa masu zaman kansu (CPPE), Muda Yusuf, ya ce, babban matsalar da ke janyo tsadar kayan abincin shi ne, jan kafar aiwatar da cire harajin shigo da kayan abincin.

A cewarsa, akwai babbar matsala tsakanin sanar da wani shiri da aiwatar da shiri a wannan gwamnati, wanda kuma bai kamata ake samun irin wannan matsalar ba.

Ya tabbatar da cewa daga kafa ga shigo da kayayyakin abincin bai samu aiwatarwa yadda ya dace ba, don haka ne ake samun karin matsala ga tattalin arziki na kasar.

Yusuf ya bukaci gwamnati ta tashi tsaye ta aiwatar da wannan shirin nata domin a samu saukin matsin rayuwa da tsadar kayayyakin abinci da jama’a ke fuskanta a halin yanzun.

Shi ma nasa bangaren, Olufemi Kayode, mamba a kungiyar samar da lasisi na kwastam a Nijeriya (ANLCA), ya ce, har yanzu babu cikakken tsarin janye harajin shigo da kayayyakin.

Ya nuna cewa akwai matsala a tsakanin tsarin sanarwar janyewar da kuma manufar aiwatar da shirin daga wajen kwastam. Don haka ne ya nuna cewa akwai bukatar daga ma’aikatar kudi da kwastam da su samar da manufa ta yadda za a aiwatar da janye harajin domin shigo da kayayyakin ba tare da wani kalubale ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamshin Jiki Da Cikar Hankalin Manzon Allah (SAW)

Next Post

Nijeriya Na Bukatar Kujeran Dindindin A Kwamitin Tsaro Na MDD – Ministan Tsaro

Related

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
Labarai

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

10 minutes ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

40 minutes ago
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

8 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

8 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

11 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

12 hours ago
Next Post
Ministan Tsaro

Nijeriya Na Bukatar Kujeran Dindindin A Kwamitin Tsaro Na MDD – Ministan Tsaro

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.