ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Bukatar Kujeran Dindindin A Kwamitin Tsaro Na MDD – Ministan Tsaro

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 years ago
Ministan Tsaro

Nijeriya ta gabatar da bukatarta na neman cikakken wakilci na didindin a kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.

Ta ce, ta bayar da gagarumin gudunmawa har sau akalla 41 a yayin gudanar da aikin wanzar da zaman lafiya a fadin duniya, kuma ta tura dakarun ta sojin Nijeriya su sama da 200,000 a ayyukan Majalisar Dinkin Duniya, don haka ta ce, ta cancanci a ba ta kujerar dindindin a kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.

  • Jihar Kano Ta Musanta Zargin Karɓar Bashin Biliyan 177 Daga Faransa
  • An Kashe Jagororin ‘Yan Bindiga, Sani Black Da Kachalla Makore A Zamfara

Ministan tsaron Nijeriya, Mohammed Badaru, shi ne ya nuna wannan bukatar a yayin da yake jawabi a babban taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 79 da ya gudana a New York na Amurka ranar Lahadi.
“Nijeriya na kira ga yin garambawul ga kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ta yadda za a bai wa Afrika wakilci na dindindin domin shigo da kowani bangare cikin sha’anin wanzar da zaman lafiya da tsaro a fadin duniya.”

ADVERTISEMENT

Badaru wanda ke magana a wajen taron tattauna yadda za a shigo da kowani bangare wajen kyautata zaman lafiya da tsaro a duniya. Ya ce muddin aka amince da bukatar nasu, za a kara samun wakilci wajen kyautata lamuran tsaro a Nahiyar Afirka.

Kwamitin tsaro dai na daga cikin muhimman bangarori 6 da suka hada Majalisar Dinkin Duniya. Yana da mambobin dindindin guda 15 da suke da alhakkin wanzar da zaman lafiya da tsaro a duniya, bayar da shawarar sabbin mambobin ga babban taron majalisar, amincewa da sauye-sauyen ga yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

An kafa kwamitin tsaron da nufin wanzar da ayyukan zaman lafiya da sanya takunkumi da kula da ayyukan sojoji.

A taron, ministan tsaron ya ce, “Nijeriya ta himmatu wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin duniya, tun lokacin da ta fara tura dakarunta na soji zuwa Congo a 1960, domin kwantar da tarzoma.
“Zuwa yau, Nijeriya ta ba da gudunmawarta wajen wanzar da zaman lafiya har sau 41 a ayyukan wanzar da zaman lafiya a fadin duniya, tare da amfani da sojoji sama da 200,000 a ayyukan wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya.

“A ayyukan shiyya kuwa, Nijeriya ta taka rawa wajen gudanar da ayyukan wanzar da zaman lafiya a Cote d’Iboire, Guinea-Bissau, Gambia, Liberia, Mali, Sudan da Sierra Leone, da sauran kasashen, kuma ta bayar da gudunmawar kudade, kayan aiki, kwararrun soji, da hakan ya kaita ga zama kasa da ta fi kowace kasa bayar da gudunmawar soji da ‘yansanda a ayyukan Majalisar Dinkin Duniya.”

Shi kuma a nasa bangaren, ministan kula da harkokin kasashen waje, Yusuf Tuggar, ya yi kira ne ga shugabannin kasashen duniya da su bayar da kula wajen daurewar ci gaba, musamman a Nahiyar Afirka.
Tuggar ya bukaci kasashen da suka ci gaba da cika alkawuran da suka dauka na tallafa wa yankin Kudancin Duniya, yana mai jaddada cewa rashin cimma manufofin muradin karni ya kamata a tsawaita wa’adin shekarar 2030.

Ya kuma ba da shawarar sake yin kwaskwarima ga tsarin hada-hadar kudi na kasa da kasa domin tabbatar da gaskiya da rikon amana, tare da daukar kwararan matakai na yafe basussuka domin rage matsin tattalin arziki da kasashen Afirka ke fuskanta.

Ministan Tsaro
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Ministan Tsaro
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
NBS

Sama Da ‘Yan Nijeriya Miliyan 4 Suka Yi Zaman Kashe Wando A 2023 –NBS

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.