ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Bukatar Kujeran Dindindin A Kwamitin Tsaro Na MDD – Ministan Tsaro

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 years ago
Ministan Tsaro

Nijeriya ta gabatar da bukatarta na neman cikakken wakilci na didindin a kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.

Ta ce, ta bayar da gagarumin gudunmawa har sau akalla 41 a yayin gudanar da aikin wanzar da zaman lafiya a fadin duniya, kuma ta tura dakarun ta sojin Nijeriya su sama da 200,000 a ayyukan Majalisar Dinkin Duniya, don haka ta ce, ta cancanci a ba ta kujerar dindindin a kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.

  • Jihar Kano Ta Musanta Zargin Karɓar Bashin Biliyan 177 Daga Faransa
  • An Kashe Jagororin ‘Yan Bindiga, Sani Black Da Kachalla Makore A Zamfara

Ministan tsaron Nijeriya, Mohammed Badaru, shi ne ya nuna wannan bukatar a yayin da yake jawabi a babban taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 79 da ya gudana a New York na Amurka ranar Lahadi.
“Nijeriya na kira ga yin garambawul ga kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ta yadda za a bai wa Afrika wakilci na dindindin domin shigo da kowani bangare cikin sha’anin wanzar da zaman lafiya da tsaro a fadin duniya.”

ADVERTISEMENT

Badaru wanda ke magana a wajen taron tattauna yadda za a shigo da kowani bangare wajen kyautata zaman lafiya da tsaro a duniya. Ya ce muddin aka amince da bukatar nasu, za a kara samun wakilci wajen kyautata lamuran tsaro a Nahiyar Afirka.

Kwamitin tsaro dai na daga cikin muhimman bangarori 6 da suka hada Majalisar Dinkin Duniya. Yana da mambobin dindindin guda 15 da suke da alhakkin wanzar da zaman lafiya da tsaro a duniya, bayar da shawarar sabbin mambobin ga babban taron majalisar, amincewa da sauye-sauyen ga yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

An kafa kwamitin tsaron da nufin wanzar da ayyukan zaman lafiya da sanya takunkumi da kula da ayyukan sojoji.

A taron, ministan tsaron ya ce, “Nijeriya ta himmatu wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin duniya, tun lokacin da ta fara tura dakarunta na soji zuwa Congo a 1960, domin kwantar da tarzoma.
“Zuwa yau, Nijeriya ta ba da gudunmawarta wajen wanzar da zaman lafiya har sau 41 a ayyukan wanzar da zaman lafiya a fadin duniya, tare da amfani da sojoji sama da 200,000 a ayyukan wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya.

“A ayyukan shiyya kuwa, Nijeriya ta taka rawa wajen gudanar da ayyukan wanzar da zaman lafiya a Cote d’Iboire, Guinea-Bissau, Gambia, Liberia, Mali, Sudan da Sierra Leone, da sauran kasashen, kuma ta bayar da gudunmawar kudade, kayan aiki, kwararrun soji, da hakan ya kaita ga zama kasa da ta fi kowace kasa bayar da gudunmawar soji da ‘yansanda a ayyukan Majalisar Dinkin Duniya.”

Shi kuma a nasa bangaren, ministan kula da harkokin kasashen waje, Yusuf Tuggar, ya yi kira ne ga shugabannin kasashen duniya da su bayar da kula wajen daurewar ci gaba, musamman a Nahiyar Afirka.
Tuggar ya bukaci kasashen da suka ci gaba da cika alkawuran da suka dauka na tallafa wa yankin Kudancin Duniya, yana mai jaddada cewa rashin cimma manufofin muradin karni ya kamata a tsawaita wa’adin shekarar 2030.

Ya kuma ba da shawarar sake yin kwaskwarima ga tsarin hada-hadar kudi na kasa da kasa domin tabbatar da gaskiya da rikon amana, tare da daukar kwararan matakai na yafe basussuka domin rage matsin tattalin arziki da kasashen Afirka ke fuskanta.

Ministan Tsaro
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Ministan Tsaro
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
NBS

Sama Da ‘Yan Nijeriya Miliyan 4 Suka Yi Zaman Kashe Wando A 2023 –NBS

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.