ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jarumai A Masana’antar Kannywood Sun Jajanta Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
Jarumai

Yayin da ake ci gaba da kirga asarori da rayukan da aka rasa sakamakon wata mummunar ambaliya da aka yi a birnin Maiduguri fadar gwamnatin Jihar Borno, mutane da dama na nuna alhini da tausayawa ga wadannan mutane da abin ya shafa.

Daga cikin masu wannan jajantawa akwai jarumai a masana’antar Kannywood wadanda suka nuna alhini a bayyane suka kuma jajantawa gwamnati da kuma al’ummar jahar Borno.

  • Sama Da Kasashe Da Hukumomin Kasa Da Kasa 70 Sun Ba Da Tabbacin Halartar Bikin CIIE Karo Na 7
  • Zargin Yi Wa Almajiri Fyade: Masu Kare Hakkin Dan’adam Sun Sake Shigar Da Kara

Ali Nuhu

ADVERTISEMENT

Jarumai

Daga cikin jaruman da suka jajanta wa al’ummar Jihar Borno akwai shugaban hukumar Fina-finai ta Nijeriya kuma jarumi a masana’antar Kannywood Ali Nuhu Muhammad inda ya ce “Ina mika sakon jaje da kuma alhini ga mutanen da ambaliyar ruwa ya shafa a Jahar Borno da sauran yankunan kasar nan, Allah ya kawo mana saukin wannan al’amarin”.

LABARAI MASU NASABA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

Abba El Mustapha

Jarumai

 

Haka zalika akwai shugaban hukumar ta ce fina finai da dab’i na jahar Kano Abba El Mustapha shima ya jajantawa wadannan bayin Allah da ambaliyar ruwa ta shafa,a wani rubutu da ya yi a shafinsa na Facebook El Mustapha ya ce “Wallahi, da garin MAIDUGURI na Kwana na kuma tashi a raina. Ya Allah ka kawo musu mafuta ta ALHERI kasa IBTILA’IN da ya faru dasu ya zama kaffara”.

Sani Musa Danja

Akwai kuma jarumi kuma tsohon dan takarar shugaban karamar hukumar Nassarawa da ke Jihar Kano Sani Musa Danja inda a wani faifan bidiyo da aka dora a shafukan zumunta ya ke cewa a madadin masana’antar Kannywood ya na jajantawa al’ummar birnin Maiduguri da ma jahar Borno baki daya, ya na fatan duk wadanda suka rasa dukiyoyins Allah ya mayar masu da mafificin alheri.

Aminu Ladan Abubakar (ALA)

Jarumai

Daya daga cikin dattawan mawaka a masana’antar Kannywood Aminu Ladan Abubakar wanda akafi sani da Ala shima ba a barshi a baya ba wajen jajantawa wadannan bayin Allah da iftila’in ruwa ya shafa,inda ya roki Allah ya gafarta wa wazanda suka rasa rayukansu ya kuma mayar da alheri ga mutanen da suka yi asarar dukiyoyinsu.

Dauda Kahutu Rarara

Jarumai

Mawakin siyasa Dauda Kahutu Rarara na daga cikin wadanda suka bayar da gudunmawar addu’a da kuma aljihunsu,Rarara ya jajantawa al’ummar jahar Borno da kuma mutanen Maiduguri da abin ya shafa,haka zalika ya bayar da gudunmawar abinci da sauran kayan amfani ga wani rukuni na masu gudun hijira a Maiduguri.

Jarumai
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Za’a Dakatar Da Wasa A Farkon Minti 10 Na Kowane Wasa A Kasar Argentina Saboda Girmama Messi
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Ahanor Kan Fam Miliyan 40

MASU ALAKA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
Jarumai
Nishadi

Dalilan Da Suka Sa Ba Zan Iya Auren Ɗan Film Ba —Bilkisu Bishasha

August 23, 2026
Next Post
Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?

Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.