• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karin Harajin Amurka Ba Zai Dakile Sashen Kere-Keren Kasar Sin Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Karin Harajin Amurka Ba Zai Dakile Sashen Kere-Keren Kasar Sin Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A baya bayan nan bangaren kasar Amurka na ci gaba da aiwatar da matakai daban daban na karin haraji kan hajojin kasar Sin dake shiga Amurka, musamman hajojin da suka shafi na manyan fasahohi, da ababen hawa masu hade da yanar gizo, da karafa da dangoginsu, matakin da masharhanta ke kallo a matsayin wata dabara da kokarin dakile ci gaban masana’antun kere-kere na Sin, duk da cewa hakan ba Sin din kadai zai illata ba, har ma da tattalin arzikin ita kanta Amurka.

 

A baya bayan nan, an ga yadda gwamnatin Amurka ta ayyana manufar kara haraji kan irin wadannan hajoji, ciki har da karin harajin kaso 100 kan ababen hawa masu aiki da lantarki ko EVs kirar kasar Sin, da karin kaso 50 bisa dari kan sassan na’urar samar da lantarki ta amfani da hasken rana ko solar, da karin kaso 25 bisa dari kan karafa da goran ruwa, da batiran EVs, da sauran wasu sanadarai masu nasaba, manufar da a cewar ofishin wakilcin cinikayya na Amurka za ta fara aiki tun daga ranar Juma’a 27 ga watan nan.

  • Sin Na Adawa Da Matsayin Amurka Na Shirin Dakatar Da Amfani Da Ababen Hawa Dake Hade Da Yanar Gizo Kirar Sin
  • Sin Ta Kira Taron Nazarin Yanayi Da Aikin Raya Tattalin Arzikin Kasar 

Har kullum ’yan siyasar Amurka na amfani da batun karin haraji, da sauran karin matakan baiwa kasuwar gida kariya, a matsayin makamin dakile kasar Sin ta fuskar takarar cinikayya. To sai dai kuma irin wadannan matakai sun ci karo da kyakkyawan tunani na cimma nasarar raya cinikayya, da bunkasa tattalin arziki tsakanin kasashen duniya.

 

Labarai Masu Nasaba

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Tuni kasar Sin ta samar da tsari mai juriya na raya fannin kere-kere, wanda ke dogaro ga tarin basirar dake cikin kasar, da babbar kasuwar ta mai yalwa, don haka ba ta dogaro ga neman alfarmar wata kasa dake ketare wajen cimma burinta na raya kai.

 

Hakan na iya kara bayyana a fili, idan muka kalli kwarya-kwaryar rahoton da hukumar lura da ikon mallakar fasaha ta kasa da kasa ta fitar game da alkaluman kere-kere na duniya ko (GII) na shekarar 2024, wadanda suka nuna cewa, Sin na da tarin cibiyoyin kere-keren kimiyya da fasaha har 26, cikin jimillar 100 dake kan gaba a duniya, ta kuma tabbatar da matsayinta na jagora a duniya a wannan fanni a tsawon shekaru 2 a jere.

 

Ko shakka babu matakan baiwa kasuwa kariya ba za su warware ginshikan matsalo da kasar Amurka ke fuskanta ba, musamman a fannin takara tsakanin masana’antu. Kuma ta hanyar dora laifi ga kasar Sin, Amurka na kaucewa sahihan matakai da ya kamata ta dauka na bunkasa tattalin arzikinta. Don haka lokaci ya yi da Amurka za ta yi karatun ta nutsu, ta yi hangen nesa, tare da karkata akala zuwa ga sauye-sauye a cikin gida, da zakulo hanyoyin raya kai, maimakon baiwa kasuwa kariya, ko yin fito na fito da kasar Sin. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Batun Amfani Da Na’urori Masu Basira A Fannin Watsa Labarai Na Sin Na 2024

Next Post

An Kashe Jagororin ‘Yan Bindiga, Sani Black Da Kachalla Makore A Zamfara

Related

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya
Daga Birnin Sin

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

12 hours ago
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

13 hours ago
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 
Daga Birnin Sin

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

13 hours ago
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya
Daga Birnin Sin

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

15 hours ago
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

16 hours ago
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 
Daga Birnin Sin

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

18 hours ago
Next Post
Sojoji

An Kashe Jagororin 'Yan Bindiga, Sani Black Da Kachalla Makore A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.