ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karin Harajin Amurka Ba Zai Dakile Sashen Kere-Keren Kasar Sin Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Amurka

A baya bayan nan bangaren kasar Amurka na ci gaba da aiwatar da matakai daban daban na karin haraji kan hajojin kasar Sin dake shiga Amurka, musamman hajojin da suka shafi na manyan fasahohi, da ababen hawa masu hade da yanar gizo, da karafa da dangoginsu, matakin da masharhanta ke kallo a matsayin wata dabara da kokarin dakile ci gaban masana’antun kere-kere na Sin, duk da cewa hakan ba Sin din kadai zai illata ba, har ma da tattalin arzikin ita kanta Amurka.

 

A baya bayan nan, an ga yadda gwamnatin Amurka ta ayyana manufar kara haraji kan irin wadannan hajoji, ciki har da karin harajin kaso 100 kan ababen hawa masu aiki da lantarki ko EVs kirar kasar Sin, da karin kaso 50 bisa dari kan sassan na’urar samar da lantarki ta amfani da hasken rana ko solar, da karin kaso 25 bisa dari kan karafa da goran ruwa, da batiran EVs, da sauran wasu sanadarai masu nasaba, manufar da a cewar ofishin wakilcin cinikayya na Amurka za ta fara aiki tun daga ranar Juma’a 27 ga watan nan.

ADVERTISEMENT
  • Sin Na Adawa Da Matsayin Amurka Na Shirin Dakatar Da Amfani Da Ababen Hawa Dake Hade Da Yanar Gizo Kirar Sin
  • Sin Ta Kira Taron Nazarin Yanayi Da Aikin Raya Tattalin Arzikin Kasar 

Har kullum ’yan siyasar Amurka na amfani da batun karin haraji, da sauran karin matakan baiwa kasuwar gida kariya, a matsayin makamin dakile kasar Sin ta fuskar takarar cinikayya. To sai dai kuma irin wadannan matakai sun ci karo da kyakkyawan tunani na cimma nasarar raya cinikayya, da bunkasa tattalin arziki tsakanin kasashen duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

Tuni kasar Sin ta samar da tsari mai juriya na raya fannin kere-kere, wanda ke dogaro ga tarin basirar dake cikin kasar, da babbar kasuwar ta mai yalwa, don haka ba ta dogaro ga neman alfarmar wata kasa dake ketare wajen cimma burinta na raya kai.

 

Hakan na iya kara bayyana a fili, idan muka kalli kwarya-kwaryar rahoton da hukumar lura da ikon mallakar fasaha ta kasa da kasa ta fitar game da alkaluman kere-kere na duniya ko (GII) na shekarar 2024, wadanda suka nuna cewa, Sin na da tarin cibiyoyin kere-keren kimiyya da fasaha har 26, cikin jimillar 100 dake kan gaba a duniya, ta kuma tabbatar da matsayinta na jagora a duniya a wannan fanni a tsawon shekaru 2 a jere.

 

Ko shakka babu matakan baiwa kasuwa kariya ba za su warware ginshikan matsalo da kasar Amurka ke fuskanta ba, musamman a fannin takara tsakanin masana’antu. Kuma ta hanyar dora laifi ga kasar Sin, Amurka na kaucewa sahihan matakai da ya kamata ta dauka na bunkasa tattalin arzikinta. Don haka lokaci ya yi da Amurka za ta yi karatun ta nutsu, ta yi hangen nesa, tare da karkata akala zuwa ga sauye-sauye a cikin gida, da zakulo hanyoyin raya kai, maimakon baiwa kasuwa kariya, ko yin fito na fito da kasar Sin. (Saminu Alhassan)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
  • Sulaiman
    Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

MASU ALAKA

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
Daga Birnin Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026
Next Post
Sojoji

An Kashe Jagororin 'Yan Bindiga, Sani Black Da Kachalla Makore A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.