• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar ‘Yanci: Jihar Kano Ta Zama Madubin Dubawa A Kan Kyakkyawan Shugabanci – Gwamna Abba

by Abdullahi Muh'd Sheka
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Ranar ‘Yanci: Jihar Kano Ta Zama Madubin Dubawa A Kan Kyakkyawan Shugabanci – Gwamna Abba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kano ta shirya taron ƙara wa juna sani a wani ɓangare na bukukuwan cikar ƙasar nan shekara 64 da samun ‘yancin kai.

Taron wanda ya mayar da hankali kan irin ci gaban da aka samu da ƙalubalen da ke addabar ƙasar nan, ya gudana ne a ɗakin taro na fadar Gwamnatin Kano (Coronation Hall).

Da yake jawabi, Gwamnan Jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya taɓo batutuwa masu motsa zuciya, inda ya bayyana cewa bisa sake fasalin shugabanci da tabbatar da riƙon amana, Jihar Kano ta zama madubi ga jihohi da kuma fagen ci gaban siyasar ƙasar nan.

  • NAPTIP Ta Kuɓutar Da Yara 19 Da Aka Sace A Kebbi 

Gwamna Abba Kabir Yusuf bayan jinjina wa ƙoƙarin kwamitin da ya tsara wannan taro wanda ya ce ya yi kyakkyanwan hange da tunanin zaƙulo masu gabatar da jawabai waɗanda suka kasance mutane masu kima da daraja, ya yi ƙarin haske kan kyakkyawan salon shugabancin gwamnatinsa.

Ya ce gwamnatin ta mayar da hankali sosai kan wasu muhimman ayyuka da suke da alaƙa da kyautata rayuwar al’ummar Jihar Kano kai-tsaye.
“Zan yi amfani da wannan dama domin bayyana wasu daga cikin manyan nasarorin da Gwamnatin Kano ta samu a ɓangarori daban-daban, wannan kuma wani ƙoƙari ne na magance ƙalubalen da ya jima yana addabar rayuwar mazauna Kano.

Labarai Masu Nasaba

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

‘A ɓangaren ilimi mun samu gagarumar nasarar sake farfaɗo da sashin, hakan ya haɗa da ginawa tare da gyaran makarantu, ɗaukar ƙwararrun malamai, samar da kayan koyo da koyarwa, haka kuma mun bujiro da tsarilimantarwa ta hanyar fasahar zamani da koyar da sana’o’i ga matasa.

“Sashin lafiya na cikin ɓangarorin da wannan gwamnati ke bai wa kulawa ta musamman, ta yadda aka ɗaga darajar cibiyoyin kiwon lafiya, da kyautata tsarin kula da lafiyar mata masu ciki da yara ƙanana, kana an kuma yi duk mai yiwuwa wajen ganin ba a bar jama’ar karkara a baya ba. Sai kuma yadda muka tunkari ƙalubalen cututtuka kamar maleriya, ƙarancin abinci mai gina jiki da sauran cututtukaka masu yaɗuwa.”

Har ila yau, Gwamna Abba Kabir ya nunar da cewa, sauran ɓangarorin da ke samun kyakkyawar kulawa a gwamnatinsa sun haɗa da sashin noma, Tsaro, Tallafa wa matasa da jari iri daban-daban, inganta tsarin aikin gwamnati da bayar da fifiko wajen biyan basussukan kuɗaɗen fansho da aka danne wa masu su tsawon lokaci.

Gwamnan ya kuma bayyana irin gagarumar nasarar da suka samu ta fuskar manyan ayyuka kamar kyautata muhalli, inganta harkar wasanni waɗanda suka samar wa Jihar Kano gagarumin ci gaba.

Daganan sai Gwamna Abba Kabir ya jaddada buƙatar haɗin kai a tsakanin al’ummar Jihar Kano domin ƙara samun nasarar da ake fata, yana mai cewar, “wannan kuma bai zai samu ba sai ta hanyar jajircewa, sadaukar da kai domin kare kimar al’ummar mu.” In ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci GabaGwamna Abba Gida-gidaGwamna Abba Kabirkano
ShareTweetSendShare
Previous Post

MƊD Ta Ƙaddamar Da Shirin “Muryoyi Daga Sahel” Karo Na Biyu

Next Post

‘Yancin Kai: PDP Ta Bukaci Tinubu Ya Rage Kudin Man Fetur

Related

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 
Manyan Labarai

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

40 minutes ago
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

20 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

2 days ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

2 days ago
Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu
Manyan Labarai

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

2 days ago
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye
Manyan Labarai

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

2 days ago
Next Post
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

‘Yancin Kai: PDP Ta Bukaci Tinubu Ya Rage Kudin Man Fetur

LABARAI MASU NASABA

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

August 4, 2025
Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.