• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ahmad Musa Da Shehu Abdullahi Sun Koma Kano Pillars Da Taka Leda

by Abba Ibrahim Wada
12 months ago
in Wasanni
0
Ahmad Musa Da Shehu Abdullahi Sun Koma Kano Pillars Da Taka Leda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, ta tabbatar da cewa tsofaffin ƴan wasanninta, Ahmad Musa da Shehu Abdullahi sun koma ƙungiyar domin buga kakar wasa ta 2024 zuwa 2025. 

A wata sanarwa da mai magana da yawun kungiyar, Abubakar Isa Ɗandago, ya fitar a shafinsa na Facebook, ya ce ƴan wasan guda biyu sun koma ƙungiyar kuma an kammala musu rijista domin fara buga wasa.

  • Sin Na Yayata Adalci Da Dabarun Warware Takaddamar Cinikayya A Matakin Kasa Da Kasa
  • Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (8)

Ahmad Musa, mai shekara 31 a duniya ya buga wasa a kungiyar karo biyu a baya, inda ya wakilci Kano Pillars a kakar wasa ta 2009 zuwa 2010 da kuma shekara ta 2021.

Shehu Abdullahi kuma, dan asalin Jihar Sakkwato, wanda ba shi da kungiya tun shekarar 2023, ya buga wasa a kungiyar a shekara ta 2012.

Zakarun gasar Firimiyar Nijeriya, Rangers international, sun nemi daukar dan wasa Ahmad Musa, sai dai tsohon kyaftin ɗin na Super Eagles ta Nijeriya, ya fi son buga wa Kano Pillars wasa.

Labarai Masu Nasaba

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

A kakar wasan Ahmed Musa ta farko a Kano Pillars a Shekarar 2009, ya lashe kyautar wanda ya fi zura kwallo a raga a gasar Firimiyar  Nijeriya, inda ya kammala gasar da kwallaye 18 Wanda hakan ne ya ja hankalin kungiyar VVV Venlo ta kasar Netherlands ta ɗauke shi.

Sannan ya buga wasa a kungiyoyin CSKA Moscow ta kasar Rasha da Leceister City ta Ingila sai kuma Al Nassr ta kasar Saudiyya.

Ana saran Ahmad Musa da Shehu Abdullahi za su buga wasan Kano Pillars na ranar Lahadi da Sunshines Stars.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan WasaAhmed MusaKano PillarsShehu Abdullahi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Yayata Adalci Da Dabarun Warware Takaddamar Cinikayya A Matakin Kasa Da Kasa

Next Post

Yadda Rayuwa Take A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Nijeriya

Related

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or
Wasanni

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

8 hours ago
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya
Wasanni

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

11 hours ago
Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya
Wasanni

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

13 hours ago
Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya
Wasanni

Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya

1 day ago
PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai
Wasanni

PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai

3 days ago
Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 
Wasanni

Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 

4 days ago
Next Post
Yadda Rayuwa Take A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Nijeriya

Yadda Rayuwa Take A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.