• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfanin Zogale 18 Ga Lafiyar Jikin Dan’adam

by Sani Anwar and Sulaiman
9 months ago
in Kiwon Lafiya
0
Amfanin Zogale 18 Ga Lafiyar Jikin Dan’adam
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana harkokin lafiyar abinci, sun bayyana amfanin da ganyen zogale ke da shi a jikin Dan’adam, sakamakon sinadarin da yake kunshe da su.

Har ila yau, bincike ya tabbatar da cewa; zogale itace ne mai matukar albarka, domin kuwa ya kan fito har a wurin da babu ruwa.

Don haka, ganyensa da sassakensa; na da matukar amfani a jikin mutum. Sannan kuma, yana da dauke da sinadarin A.B.C.D har ma da E, kana kuma yana dauke da sinadarin calcium da potassium, kana kuma mansa yana cikin mayukan da suka fi tsada a duniya.

Kazalika, akwai magunguna 18 da zogale ke yi ga lafiyar Dan’adam kamar haka:

– Ana dafa ganyen zogale da zuma a sha kamar shayi, domin maganin Olsa (Ulcer).

Labarai Masu Nasaba

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

– Ana kuma shafa danyen ganyen zogale a kan goshi, don maganin ciwon kai.

– Haka nan, ga wanda ya ji wani rauni ko sara; idan ya shafa danyen ganyen zogale, jinin zai tsaya nan take da izinin Allah.

– Ga mai fama da kurajen jiki, sai ya hada garin zogale da man zaitun; ya rika shawa.

– Ana kuma zuba garin zogale a kan gyambo ko wani rauni, domin ya yi saurin warke.

– Sanya garin zogale a cikin abinci, na maganin hawan jini da kuma kara wa mutum kuzari,

– Ana dafa ganyen zogale, a saka kanwa ‘yar kadan; don maganin shawara.

– Ga mai fama da ciwon ido, zai rika diga ruwan danyen zogale; haka nan shi mai fama da ciwon kunne.

– Macen da ke shayarwa kuma, ta dafa furen zogale da zuma; domin samun karin yawan ruwan nono.

– Wanda ke fama da yawan fitsari ko ciwon Siga, sai ya rika shan furen zogale da citta kamar shayi.

– Kazalika, cin zogalen ma a haka; na maganin tsutsar ciki, musamman ga yara.

– Ana daka ganyen zogale da ‘ya’yan baure a sha da nono ko kunu, domin kuwa yana maganin ciwon hanta.

– Ga mai fama da sanyin kashi ko wani kumburi, sai ya soya ‘ya’yan zogale ya daka su; ya kuma hada da man kwakwa (man- ja) sai ya rika shafawa.

– A daka zangarniyar zogale da ‘ya’yan da ke ciki da kaninfari, citta, masoro da kuma kimba, domin karin karfin namiji, sannan yana kara wa mata nishadi.

– A daka saiwar zogale da ‘ya’yan kankana a sha a nono, yana maganin tsakuwar ciki (Apendis).

– Haka nan, yana maganin typhoid, maleriya, basir da shawara; ta hanyar yawan shan ruwan dafaffen zogale.

– Kazalika, zogale na rage radadin ciwon HIB ta hanyar shan dafaffen ruwan zogalen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dole Matasanmu Su Rungumi Kasuwanci Na Zamani – Firdausi Dahiru

Next Post

Ƙungiyar Malamai Ta Ƙasa Ta Karrama Gwamna Yusuf Da Lambar Yabo

Related

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
Kiwon Lafiya

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

2 days ago
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

4 days ago
Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 
Kiwon Lafiya

Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 

1 week ago
Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?
Kiwon Lafiya

Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

3 weeks ago
Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
Kiwon Lafiya

Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

4 weeks ago
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa
Kiwon Lafiya

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

1 month ago
Next Post
Ƙungiyar Malamai Ta Ƙasa Ta Karrama Gwamna Yusuf Da Lambar Yabo

Ƙungiyar Malamai Ta Ƙasa Ta Karrama Gwamna Yusuf Da Lambar Yabo

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

July 9, 2025
Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal

Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal

July 9, 2025
Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho

Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho

July 9, 2025
Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata

Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata

July 9, 2025
Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

July 9, 2025
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

July 9, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.