• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Bukaci A Yi Bincike Tare Da Hukunta Wadanda Suka Kai Wa Motocin Kamfanin Kasar Hari A Pakistan

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

Kasar Sin ta yi Allah wadai da harin ta’addancin da aka kai a Pakistan, wanda ya yi sanadin mutuwar Sinawa biyu da ma wasu ‘yan kasar Pakistan. Haka kuma ta jajantawa wadanda suka jikkata, da ma iyalan wadanda suka rasa rayukansu. 

 

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin ne ya bayyana haka a yau, lokacin da yake amsa tambaya game da harin da aka kai wa motocin wani kamfanin kasar Sin a Pakistan, a jiya Lahadi.

  • Darajar Masana’antun Samar Da Kayayyakin Sadarwa Na Laturoni Ta Sin Ta Karu Da 13.1% A Watanni Takwas Na Farkon Bana 
  • Shugabannin Sin Da Korea Ta Arewa Sun Taya Juna Murnar Cikar Dangantakar Diplomasiyyar Kasashensu Shekaru 75 Da Kulluwa

A cewar kakakin, Sin na bukatar Pakistan ta yi dukkan kokarin da ya kamata domin jinyar wadanda suka jikkata tare da aiwatar da cikakken bincike don kama wadanda ke da hannu da kuma tabbatar da sun fuskanci fushin doka.

 

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ya kara da cewa, kasar Sin za ta ci gaba da goyon bayan Pakistan wajen inganta ayyukan yaki da ta’addanci, kuma a shirye take ta hada hannu da Pakistan din wajen dakile duk wani yunkuri na lalata dangantakar dake tsakaninsu.

 

Kafin wannan, rahotanni sun nuna cewa, wani harin ta’addanci a birnin Karachi mai tashar ruwa a kasar Pakistan, ya yi sanadin mutuwar Sinawa biyu da jikkatar wani guda, baya ga ‘yan kasar Pakistan da dama da suka mutu da kuma jikkata sanadin harin na jiya Lahadi da dare.

 

Ofishin jakadancin Sin ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa, inda ya kara da cewa, harin ya auku da misalin karfe 11 na dare a jiya Lahadi, lokacin da ‘yan ta’adda da suka kai hari kan jerin gwanon motoci daga kamfanin tashar lantarki ta Qasim a kusa da filin jirgin saman kasa da kasa na Jinnah na birnin Karachi, fadar mulkin lardin Sindh dake kudancin kasar Pakistan.

 

Gobarar da ta tashi bayan fashewar wani abu a jiyan, ta kuma shafi motoci da dama a kusa da filin jirgin na Karachi. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
Daga Birnin Sin

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Daga Birnin Sin

Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 2, 2025
Next Post
An Kashe Dorinar Ruwa A Jihar Kebbi Bayan Ta Kashe Mai-Gadin Lambun Basarake

An Kashe Dorinar Ruwa A Jihar Kebbi Bayan Ta Kashe Mai-Gadin Lambun Basarake

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.