• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara 20 Da Kafa Jaridar LEADERSHIP

by Leadership Hausa
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Shekara 20 Da Kafa Jaridar LEADERSHIP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekaru ashirin ba karamin abu ba ne a rayuwar mutum haka nan ma ba karamin abu ba ne a rayuwar kamfani. Abin ya fi a rayuwar jarida musamman a wajen da durkushewar jaridu ya zama abu mafi sauki fiye da kafuwarsu a wannan zamani.

Jaridu da dama da aka kafa a ‘yan shekarun da suka gabata duk sun mutu basu iya ko kai labari ba ma. Cikin abubuwan da suke kashe gidajen jarida da sauri sun hada da rashin talla daga abokan hulda, da kuma rashin sanya hannu gwamnati a harkokin jaridar ta hanyar ba jaridar kwangila.

  • Kasar Sin Ta Kakaba Takunkumai Kan Wasu Kamfanonin Amurka 3 Da Manyan Jami’ansu 10 Don Gane Da Batun Sayarwa Yankin Taiwan Makamai
  • Zan Yi Sanadin Ficewar Sakataren Gwamnatin Kano Daga NNPP – Hajiya Lami

Tsayuwar Jaridar LEADERSHIP kyam a kowane irin hali data samu kanta na nuni ga irin kokarin wanda ya kafa kamfanin, wato Sam Nda-Isiah, mutum wanda yake da hangen nesa, fafdandar zuciya, ga kuma dagiya a kan abin da ya yi Imani da shi a kai, da kuma zuciya ta rashin tsoro.

Karin maganar Turanci da ke cewa, “Oaks from little acorns grow” ya yi daidai da yadda jaridar da ta fara daga waje mai matukar karfafawa. Tana nan a cikin kwaryar Abuja kuma ta zama jarida mai matukar tasiri a harkar jaridu ba kawai a Nieriya ba har ma a fadin yankin Afirka gaba daya.

Bata faro a matsayin jaridar kullum ba. Ci gaban da aka samu ne ta hanyar LEADERSHIP Confidential ya haifar mata da wannan gaggarumar jaridar da muke kallo a yau.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

Wani abu da ya fita daban game da jaridar da wanda ya samar da ita shi ne, basu da wata alaka ta aiki amma a haka suka hadu suka samar da wannan jaridar da ta yi karko.

Banda zaman mahaifinsa dan jarida da kuma zamansa editan karamar jarida a jami’a wato Pharmacists’ Journal, wata babbar daukaka ta kawo shi harkar jarida ita ce makalar da yake rubutawa a jarida wato “Last Word da kuma Earshot”

Lokacin da ya shirya tsaf domin tattara rubuce-rubucen shi zuwa littafi wanda ya sa wa suna; Nigeria: Full Disclosure: Selected Writings on Gobernance, Democracy and Statecraft, May 1999 – March 2004, Sam, kamar yadda ake kiransa da ya samu kimanin Naira Miliyan ashirin wadda ta zama jarin da aka kafa shi kamfanin jaridar da ita.

Kamar yadda aka saba, Jaridar LEADERSHIP ta gamu da kalubale da dama wadanda suka bude hanyar zuwa ga ci gaban da jaridar ta samu zuwa yanzu. Abinda yafi daukar hankali shi ne rasuwar wanda ya samar da jaridar, Sam, a ranar 11 ga watan Disamba, 2022. Ga shi kuma har yanzu jaridar tana nan tsaye saboda kokarin masu ba kamfanin shawara, masu gudanarwa da kuma ma’aikatan kamfanin wadanda suka yi koyi da tsayin dakan wanda ya samar da kamfanin.

Marigayi Sam Nda-Isiaah mutum ne mai ra’ayoyi. Yana yawan gwada su. Duk da ya karanci fannin bayar da magani ne, ya kasance rikakken dan kasuwa. Ya shiga harkokin kasuwanci da dama. Daga harkar noma, tsaro da kuma bangaren kimiyya da fasaha. Duk wannan ya yi su ne bayan gajeren aikin da ya yi da kamfanin magani na Pfizer.

Wasu daga cikin magoya bayan shi basu yarda da tunanin shi ya shiga siyasa ba. Amma shi mutum ne da baya tsoron kalubale yana kara kaimi wajen fuskantar duk abin da ya sa a gabansa.

Wannan lokaci ne ya gwada karfin tubalin ginin kamafanin da marigayi Sam Nda-Isiaah ya samar kuma haka ya tsaya kyam. Jaridar ta nuna cewa ta yi kwarin da za ta iya jure duk wani duk wani kalubale musamman daga abokan hamayyar siyasa wadanda suke son a hukunta shi domin yana so a kawo sauyi.

Lokacin da ya dawo daga harkar siyasar, ya tarar da Jaridar ta sha wahala amma bata rusuna ba. Tare da sauran ma’aikata suka hada hannu suka gyara jaridar ta dawo inda ya kamata ta zama a koda yaushe.

Abubuwan alkhairin sa sun ci gaba kamar yana raye. Hakan ya faru ne saboda ya tafi ya bar mutane wadanda suka yarda da shi kuma suna nan sun yarda da shi, bugu da kari kuma a shirye suke su ci gaba daga inda ya tsaya, karkashin jagorancin shugabar kungiyar, matar shi kuma wacce ta gaje shi wato Zainab Nda-Isiaah.

Bayan shekaru ashirin da samar da jaridar kuma shekara hudu bayan rasuwar wanda ya samar da jaridar, LEADERSHIP ta ci gaba da habaka, da taimakon masu karantawa, masu ba da talla, da kuma masu taimakawa a kai a kai.

Jaridar da tafi kowace tasiri tana nan tsaye domin yi wa Ubangiji da kuma kasa aiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BikiJaridaLEADERSHIPMurnaShekaru 20
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadarin Kwale-kwale A Kaiama: Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 100

Next Post

Fafutikar Makinde Da PDP Wajen Neman Mulki A 2027

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

5 hours ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

11 hours ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da É—umi-É—uminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

16 hours ago
Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Sarakuna Sun Bukaci Gwamnati Ta Canza Salo

20 hours ago
Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

1 day ago
Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja
Manyan Labarai

Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

1 day ago
Next Post
Fafutikar Makinde Da PDP Wajen Neman Mulki A 2027

Fafutikar Makinde Da PDP Wajen Neman Mulki A 2027

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga ZaÉ“en Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.