ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara 20 Da Kafa Jaridar LEADERSHIP

by Leadership Hausa
2 years ago

Shekaru ashirin ba karamin abu ba ne a rayuwar mutum haka nan ma ba karamin abu ba ne a rayuwar kamfani. Abin ya fi a rayuwar jarida musamman a wajen da durkushewar jaridu ya zama abu mafi sauki fiye da kafuwarsu a wannan zamani.

Jaridu da dama da aka kafa a ‘yan shekarun da suka gabata duk sun mutu basu iya ko kai labari ba ma. Cikin abubuwan da suke kashe gidajen jarida da sauri sun hada da rashin talla daga abokan hulda, da kuma rashin sanya hannu gwamnati a harkokin jaridar ta hanyar ba jaridar kwangila.

  • Kasar Sin Ta Kakaba Takunkumai Kan Wasu Kamfanonin Amurka 3 Da Manyan Jami’ansu 10 Don Gane Da Batun Sayarwa Yankin Taiwan Makamai
  • Zan Yi Sanadin Ficewar Sakataren Gwamnatin Kano Daga NNPP – Hajiya Lami

Tsayuwar Jaridar LEADERSHIP kyam a kowane irin hali data samu kanta na nuni ga irin kokarin wanda ya kafa kamfanin, wato Sam Nda-Isiah, mutum wanda yake da hangen nesa, fafdandar zuciya, ga kuma dagiya a kan abin da ya yi Imani da shi a kai, da kuma zuciya ta rashin tsoro.

ADVERTISEMENT

Karin maganar Turanci da ke cewa, “Oaks from little acorns grow” ya yi daidai da yadda jaridar da ta fara daga waje mai matukar karfafawa. Tana nan a cikin kwaryar Abuja kuma ta zama jarida mai matukar tasiri a harkar jaridu ba kawai a Nieriya ba har ma a fadin yankin Afirka gaba daya.

Bata faro a matsayin jaridar kullum ba. Ci gaban da aka samu ne ta hanyar LEADERSHIP Confidential ya haifar mata da wannan gaggarumar jaridar da muke kallo a yau.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Wani abu da ya fita daban game da jaridar da wanda ya samar da ita shi ne, basu da wata alaka ta aiki amma a haka suka hadu suka samar da wannan jaridar da ta yi karko.

Banda zaman mahaifinsa dan jarida da kuma zamansa editan karamar jarida a jami’a wato Pharmacists’ Journal, wata babbar daukaka ta kawo shi harkar jarida ita ce makalar da yake rubutawa a jarida wato “Last Word da kuma Earshot”

Lokacin da ya shirya tsaf domin tattara rubuce-rubucen shi zuwa littafi wanda ya sa wa suna; Nigeria: Full Disclosure: Selected Writings on Gobernance, Democracy and Statecraft, May 1999 – March 2004, Sam, kamar yadda ake kiransa da ya samu kimanin Naira Miliyan ashirin wadda ta zama jarin da aka kafa shi kamfanin jaridar da ita.

Kamar yadda aka saba, Jaridar LEADERSHIP ta gamu da kalubale da dama wadanda suka bude hanyar zuwa ga ci gaban da jaridar ta samu zuwa yanzu. Abinda yafi daukar hankali shi ne rasuwar wanda ya samar da jaridar, Sam, a ranar 11 ga watan Disamba, 2022. Ga shi kuma har yanzu jaridar tana nan tsaye saboda kokarin masu ba kamfanin shawara, masu gudanarwa da kuma ma’aikatan kamfanin wadanda suka yi koyi da tsayin dakan wanda ya samar da kamfanin.

Marigayi Sam Nda-Isiaah mutum ne mai ra’ayoyi. Yana yawan gwada su. Duk da ya karanci fannin bayar da magani ne, ya kasance rikakken dan kasuwa. Ya shiga harkokin kasuwanci da dama. Daga harkar noma, tsaro da kuma bangaren kimiyya da fasaha. Duk wannan ya yi su ne bayan gajeren aikin da ya yi da kamfanin magani na Pfizer.

Wasu daga cikin magoya bayan shi basu yarda da tunanin shi ya shiga siyasa ba. Amma shi mutum ne da baya tsoron kalubale yana kara kaimi wajen fuskantar duk abin da ya sa a gabansa.

Wannan lokaci ne ya gwada karfin tubalin ginin kamafanin da marigayi Sam Nda-Isiaah ya samar kuma haka ya tsaya kyam. Jaridar ta nuna cewa ta yi kwarin da za ta iya jure duk wani duk wani kalubale musamman daga abokan hamayyar siyasa wadanda suke son a hukunta shi domin yana so a kawo sauyi.

Lokacin da ya dawo daga harkar siyasar, ya tarar da Jaridar ta sha wahala amma bata rusuna ba. Tare da sauran ma’aikata suka hada hannu suka gyara jaridar ta dawo inda ya kamata ta zama a koda yaushe.

Abubuwan alkhairin sa sun ci gaba kamar yana raye. Hakan ya faru ne saboda ya tafi ya bar mutane wadanda suka yarda da shi kuma suna nan sun yarda da shi, bugu da kari kuma a shirye suke su ci gaba daga inda ya tsaya, karkashin jagorancin shugabar kungiyar, matar shi kuma wacce ta gaje shi wato Zainab Nda-Isiaah.

Bayan shekaru ashirin da samar da jaridar kuma shekara hudu bayan rasuwar wanda ya samar da jaridar, LEADERSHIP ta ci gaba da habaka, da taimakon masu karantawa, masu ba da talla, da kuma masu taimakawa a kai a kai.

Jaridar da tafi kowace tasiri tana nan tsaye domin yi wa Ubangiji da kuma kasa aiki.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Fafutikar Makinde Da PDP Wajen Neman Mulki A 2027

Fafutikar Makinde Da PDP Wajen Neman Mulki A 2027

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.