ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara 20 Da Kafa Jaridar LEADERSHIP

by Leadership Hausa
2 years ago

Shekaru ashirin ba karamin abu ba ne a rayuwar mutum haka nan ma ba karamin abu ba ne a rayuwar kamfani. Abin ya fi a rayuwar jarida musamman a wajen da durkushewar jaridu ya zama abu mafi sauki fiye da kafuwarsu a wannan zamani.

Jaridu da dama da aka kafa a ‘yan shekarun da suka gabata duk sun mutu basu iya ko kai labari ba ma. Cikin abubuwan da suke kashe gidajen jarida da sauri sun hada da rashin talla daga abokan hulda, da kuma rashin sanya hannu gwamnati a harkokin jaridar ta hanyar ba jaridar kwangila.

  • Kasar Sin Ta Kakaba Takunkumai Kan Wasu Kamfanonin Amurka 3 Da Manyan Jami’ansu 10 Don Gane Da Batun Sayarwa Yankin Taiwan Makamai
  • Zan Yi Sanadin Ficewar Sakataren Gwamnatin Kano Daga NNPP – Hajiya Lami

Tsayuwar Jaridar LEADERSHIP kyam a kowane irin hali data samu kanta na nuni ga irin kokarin wanda ya kafa kamfanin, wato Sam Nda-Isiah, mutum wanda yake da hangen nesa, fafdandar zuciya, ga kuma dagiya a kan abin da ya yi Imani da shi a kai, da kuma zuciya ta rashin tsoro.

ADVERTISEMENT

Karin maganar Turanci da ke cewa, “Oaks from little acorns grow” ya yi daidai da yadda jaridar da ta fara daga waje mai matukar karfafawa. Tana nan a cikin kwaryar Abuja kuma ta zama jarida mai matukar tasiri a harkar jaridu ba kawai a Nieriya ba har ma a fadin yankin Afirka gaba daya.

Bata faro a matsayin jaridar kullum ba. Ci gaban da aka samu ne ta hanyar LEADERSHIP Confidential ya haifar mata da wannan gaggarumar jaridar da muke kallo a yau.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Wani abu da ya fita daban game da jaridar da wanda ya samar da ita shi ne, basu da wata alaka ta aiki amma a haka suka hadu suka samar da wannan jaridar da ta yi karko.

Banda zaman mahaifinsa dan jarida da kuma zamansa editan karamar jarida a jami’a wato Pharmacists’ Journal, wata babbar daukaka ta kawo shi harkar jarida ita ce makalar da yake rubutawa a jarida wato “Last Word da kuma Earshot”

Lokacin da ya shirya tsaf domin tattara rubuce-rubucen shi zuwa littafi wanda ya sa wa suna; Nigeria: Full Disclosure: Selected Writings on Gobernance, Democracy and Statecraft, May 1999 – March 2004, Sam, kamar yadda ake kiransa da ya samu kimanin Naira Miliyan ashirin wadda ta zama jarin da aka kafa shi kamfanin jaridar da ita.

Kamar yadda aka saba, Jaridar LEADERSHIP ta gamu da kalubale da dama wadanda suka bude hanyar zuwa ga ci gaban da jaridar ta samu zuwa yanzu. Abinda yafi daukar hankali shi ne rasuwar wanda ya samar da jaridar, Sam, a ranar 11 ga watan Disamba, 2022. Ga shi kuma har yanzu jaridar tana nan tsaye saboda kokarin masu ba kamfanin shawara, masu gudanarwa da kuma ma’aikatan kamfanin wadanda suka yi koyi da tsayin dakan wanda ya samar da kamfanin.

Marigayi Sam Nda-Isiaah mutum ne mai ra’ayoyi. Yana yawan gwada su. Duk da ya karanci fannin bayar da magani ne, ya kasance rikakken dan kasuwa. Ya shiga harkokin kasuwanci da dama. Daga harkar noma, tsaro da kuma bangaren kimiyya da fasaha. Duk wannan ya yi su ne bayan gajeren aikin da ya yi da kamfanin magani na Pfizer.

Wasu daga cikin magoya bayan shi basu yarda da tunanin shi ya shiga siyasa ba. Amma shi mutum ne da baya tsoron kalubale yana kara kaimi wajen fuskantar duk abin da ya sa a gabansa.

Wannan lokaci ne ya gwada karfin tubalin ginin kamafanin da marigayi Sam Nda-Isiaah ya samar kuma haka ya tsaya kyam. Jaridar ta nuna cewa ta yi kwarin da za ta iya jure duk wani duk wani kalubale musamman daga abokan hamayyar siyasa wadanda suke son a hukunta shi domin yana so a kawo sauyi.

Lokacin da ya dawo daga harkar siyasar, ya tarar da Jaridar ta sha wahala amma bata rusuna ba. Tare da sauran ma’aikata suka hada hannu suka gyara jaridar ta dawo inda ya kamata ta zama a koda yaushe.

Abubuwan alkhairin sa sun ci gaba kamar yana raye. Hakan ya faru ne saboda ya tafi ya bar mutane wadanda suka yarda da shi kuma suna nan sun yarda da shi, bugu da kari kuma a shirye suke su ci gaba daga inda ya tsaya, karkashin jagorancin shugabar kungiyar, matar shi kuma wacce ta gaje shi wato Zainab Nda-Isiaah.

Bayan shekaru ashirin da samar da jaridar kuma shekara hudu bayan rasuwar wanda ya samar da jaridar, LEADERSHIP ta ci gaba da habaka, da taimakon masu karantawa, masu ba da talla, da kuma masu taimakawa a kai a kai.

Jaridar da tafi kowace tasiri tana nan tsaye domin yi wa Ubangiji da kuma kasa aiki.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Fafutikar Makinde Da PDP Wajen Neman Mulki A 2027

Fafutikar Makinde Da PDP Wajen Neman Mulki A 2027

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.