ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Ganduje

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje na kara shan matsin lamba a kan ya sauka daga mukaminsa, inda wani jigon APC, Alhaji Saleh Zazzaga ya rubuta masa wasika tare da ba shi wa’adin kwanaki 7 ya yi murabus daga mukaminsa na shugaban jam’iyyar APC.

Alhaji Zazzaga, ya kasance shugaban kungiyar ‘ya’yan jam’iyyar APC na yankin arewa ta tsakiya, sannan kuma shi mamba ne a lokacin yakin neman zaben Tinubu/Shettima, ya dai bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a garin Jos, Babban Birnin Jihar Filato.

  • Janar Gowon: Tsohon Shugaban Kasa Mafi Tsawon Rai A Nijeriya Na Cika Shekara 90
  • Majalisa Ta Amince Jami’an Kiyaye Haɗurra Su Riƙe Bindiga 

Ya ce a cikin wasikar da ya rubuta akwai dalilansa wanda ya bukaci Ganduje ya yi murabus tare da bayar da wa’adin kwanaki 7 da zai kare a ranar Litinin na mako mai zuwa, wanda ya ce zai dauki matakin shari’a.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, a babban taron jam’iyyar da aka gudanar da ranar 26 ga Maris, 2022, ya kamata a zabi dan yankin arewa ta tsakiya ne ba Ganduje da ya fito daga yankin arewa maso yamma ba.

Jigon jam’iyyar APC ya ce kasancewar Ganduje shugaban jam’iyyar hakan ya saba wa sashi na 31.5 31.5 (i) da (ib) na kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC na shekara 2022 wanda aka yi wa garanbawul, sannan kuma ya saba wa yarjejeniyar tsarin karba-karba na mukamin shugabancin jam’iyyar wanda ya kamata a bai wa yankin arewa ta tsakiya.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Ya ce wasikar tana zama wani shaida na hanyar warware rikici cikin sauki da kuma tattaunawa ta lumana, amma duk da haka Ganduje ya yi kememe ya ci gaba da zama kan mukamin da ya kamata a bai wad an asalin yankin arewa ta tsakiya.

Haka kuma Zazzaga ya yi kwafin wasikar ga Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio da shugaban majalisar wakilai, Honorabul Tajudeen Abbas da kwamitin gudanarwa na APC na kasa da kuma sashin shari’a na jam’iyyar APC.

Idan za a iya tunawa dai, kungiyar APC na yankin arewa ta tsakiya sun gurfanar da Ganduje a gaban babban kotun tarayya da ke Abuja na neman a tsige shi daga kan mukaminsa na shugaban jam’iyyar, sai dai kotun ta yi watsi da karar sakamakon wasu dalilai.

Sai dai kuma, ‘ya’yan jam’iyyar APC a yankin arewa ta tsakiya da sauran wasu jiga-jigan jam’iyyar daga yankin sun ci gaba da wannan yaki har sai hakarsu ta cimma ruwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya
Manyan Labarai

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
Next Post
CBN Ya Yi Alkawarin Kawo Karshen Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

CBN Ya Sake Nanata Ba Da Kariya Ga Kudaden Ajiya A Bankuna

LABARAI MASU NASABA

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.