ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin Farfado Da Ilimi: Gwamnan Kano Ya Zama Gwarzo A Tsakanin Gwamnoni

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
Ilimi

Gwamnan Jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf na ci gaba da karbar gwababan lambobin yabo wadda ke alamta nagarta da jajircewarsa wajen bunkasa harkokin ilimi da tsantsenin lalitar al’ummar Kano inda wannan ne babban dalilin da Kanawa ke kiransa da sunan “A kori jahilci”.

Gwamna Abba Kabir Yusuf na cikin gwamnoni shida da suka rabauta da babbar lambar yabo daga kungiyar Malamai ta Kasa tare da hadin guiwa da ma’aikatar ilimi ta Tarayya a lokacin bikin ranar malamai ta duniya da aka gudanar a babban filin taron Eagle Skuare da ke Abuja.

  • Hadarin Kwale-kwale A Kaiama: Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 100
  • Ba Mijina Ba Ne Sanadin Ƙuncin Rayuwa Da Ake Ciki A Nijeriya – Uwargidan Shugaban Ƙasa

Inda aka karrama Gwamna Abba da lamba mafi daraja bisa kyakkyawar nasarar da ya samu ta fuskar inganta harkar ilimi. Kamar yadda mai magana da yawun Gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya bayyana wa LEADERSHIP Hausa

ADVERTISEMENT

Jajircewa tare da sadaukar da kan Gwamna Abba ne ya ja hankalin kungiyar Malaman tare da hadin guiwar Ma’aikatar ilimi ta tarayya wajen zabo shi domin ba shi wannan lamba musamman matakinsa na Sanya wa harkar ilimi dokar ta-baci tare da kafa manyan kwamitoci domin magance matsalar da ta jima tana ci wa harkar ilimi a tuwo a kwarya a Kano. Musamman tsarin tallafa wa malamai tare da kyautata walwalarsu.

Wani abu da ke daukar hankalin duk wani mai rajin kishin ganin an farfado da harkar ilimi a Kano shi ne yadda gwamnan bai tsaya ilimin zamani ba kawai, har makarantun tsangayu da islamiyyu ya saka cikin jadawalin inganta harkar ilimin baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Domin ganin aniyarsa ta sake farfado da harkar ilimi ta kai inda yake fata, Gwamna Abba a kasafin kudin wannan shekara ta 2024, ya tabbatar da gabib sashin ilimi ne ya rabauta da kaso mafi tsoka domin tabbatar da cimma nasara. Musamman shirinsa na kara gina ajujuwa, zuba kayan zama da raba kayan koyo da koyarwa ga daukacin makarantun Jihar Kano.

Irin wadannan ayyuka ne Gwamna Abba ya alkawarta wa Kanawa kuma gashi tun kafin a yi rabin wa’adi kwalliya tana biya kudin sabulu.

A halin da ake ciki, tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma Jagoran Jam’iyyar NNPPFormer, Rabi’u Musa Kwankwaso ya taya Gwamna Abba Kabir Yusuf murnar samun lambar yabo mafi daraja daga Kungiyar Malaman Makaranta ta Kasa (NUT), bisa hobbasar da yake yi wajen bunkasa sashen ilimi.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a shafinsa na D (da aka fi sani da Twitter a baya), inda ya nunar da cewa hakika, Gwamna Abba ya nuna sadaukarwa ga farfado da sashen ilimi na Jihar Kano inda ya bukaci ya kara kaimi a kan hakan.

Ilimi
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.