• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Fitar Da Jaddawalin Babban Taronta Na Shiyyoyi Na 2025

by Yusuf Shuaibu
8 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
PDP Ta Fitar Da Jaddawalin Babban Taronta Na Shiyyoyi Na 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar PDP ya amince da jadawalin taron shiyoyi na 2025.

Rahotanni sun bayyana cewa za a zabi sabbin mambobin kwamitocin gudanarwa na shiyoyi da kuma shugabannin na shiyoyi a wannan babban taro.

  • Janar Gowon: Tsohon Shugaban Kasa Mafi Tsawon Rai A Nijeriya Na Cika Shekara 90
  • Babu Hannun Mijina A Wahalar Da Ƴan Nijeriya Ke Sha

A wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Abuja, mai magana da yawun jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba, ya ce kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na kasa ya amince da gudanar da taron shiyoyin.

Ya bayyana cewa kwamitin gudanarwa na jam’iyyar ya amince da jadawalin a yayin taronta na 592, gabanin karewar wa’adin shugabannin shiyoyin na Kudu maso Kudu, Kudu maso Gabas, Kudu maso Yamma, Arewa ta Tsakiya da Arewa-maso Gabas.

Sanarwar ta bayyana jadawalin ayyuka, ta ce, “Sayar da fom ga dukkan mukaman na sabbi da tsofaffin shugabannin shiyoyi na kasa a Kudu maso Kudu, Kudu maso Gabas, Kudu maso Yamma, Arewa ta Tsakiya da Arewa maso Gabas: Litinin, 18 ga Nuwamban 2024 zuwa ranar Laraba, 18 ga Disamban 2024.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

“Wa’adin karshe na miyar da fom din takara zai kasance a ranar Juma’a, 17 ga Janairun 2025.

“Tantance ‘yan takara a hedikwatar shiyya, zai kasance ranar Asabar, 25 ga Janairu, 2025.

“Amincewa da tantance ‘yan takara a hedkwatar shiyya, zai kasance ranar Asabar, 1 ga Fabrairu, 2025.

“Wallafa sunayen ‘yan takara, zai kasance ranar Laraba, 12 ga Fabrairun 2025. Buga jerin sunayen wakilai, zai kasance ranar Alhamis, 13 ga Fabrairun 2025.

“Ranakun babban taron shiyoyin na Arewa maso Gabas, Kudu maso Gabas, da Kudu maso Kudu, zai kasance ranar Asabar, 22 ga Fabrairun 2025.

“Amincewa da babban taron shiyoyin, zai kasance ranar Talata, 25 ga Fabrairu, 2025.

“Babban taron shiyoyi na shiyyar Arewa ta Tsakiya da Kudu maso Yamma, zai gudana a ranar Asabar, 22 ga Maris, 2025. Amincewa da babban taron, zai kasance ranar Laraba, 26 ga Maris, 2025.”

Jam’iyyar ta bukaci duk masu son yin takara da su tuntubi sakatariyar jam’iyyar na kasa don samun bayanai kan kudaden da ake bukata da sauran tambayoyi.

Ologunagba ya kuma ja hankalin dukkan shugabannin PDP da masu ruwa da tsaki, da ’ya’yan jam’iyyar da su ci gaba da hada kan su, su kuma yi kokarin ganin jam’iyyar ta samu ci gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: PDPShiyoyyiSiyasaTaroZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kanana Da Matsakaitan Kamfanonin Sin Sun Samu Bunkasuwa Yadda Ya Kamata

Next Post

Nijeriya Ta Doke Kasar Libya A Akwa Ibom

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

8 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Nijeriya Ta Doke Kasar Libya A Akwa Ibom

Nijeriya Ta Doke Kasar Libya A Akwa Ibom

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
PDP

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.