• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Fitar Da Jaddawalin Babban Taronta Na Shiyyoyi Na 2025

by Yusuf Shuaibu
10 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
PDP Ta Fitar Da Jaddawalin Babban Taronta Na Shiyyoyi Na 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar PDP ya amince da jadawalin taron shiyoyi na 2025.

Rahotanni sun bayyana cewa za a zabi sabbin mambobin kwamitocin gudanarwa na shiyoyi da kuma shugabannin na shiyoyi a wannan babban taro.

  • Janar Gowon: Tsohon Shugaban Kasa Mafi Tsawon Rai A Nijeriya Na Cika Shekara 90
  • Babu Hannun Mijina A Wahalar Da Ƴan Nijeriya Ke Sha

A wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Abuja, mai magana da yawun jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba, ya ce kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na kasa ya amince da gudanar da taron shiyoyin.

Ya bayyana cewa kwamitin gudanarwa na jam’iyyar ya amince da jadawalin a yayin taronta na 592, gabanin karewar wa’adin shugabannin shiyoyin na Kudu maso Kudu, Kudu maso Gabas, Kudu maso Yamma, Arewa ta Tsakiya da Arewa-maso Gabas.

Sanarwar ta bayyana jadawalin ayyuka, ta ce, “Sayar da fom ga dukkan mukaman na sabbi da tsofaffin shugabannin shiyoyi na kasa a Kudu maso Kudu, Kudu maso Gabas, Kudu maso Yamma, Arewa ta Tsakiya da Arewa maso Gabas: Litinin, 18 ga Nuwamban 2024 zuwa ranar Laraba, 18 ga Disamban 2024.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

“Wa’adin karshe na miyar da fom din takara zai kasance a ranar Juma’a, 17 ga Janairun 2025.

“Tantance ‘yan takara a hedikwatar shiyya, zai kasance ranar Asabar, 25 ga Janairu, 2025.

“Amincewa da tantance ‘yan takara a hedkwatar shiyya, zai kasance ranar Asabar, 1 ga Fabrairu, 2025.

“Wallafa sunayen ‘yan takara, zai kasance ranar Laraba, 12 ga Fabrairun 2025. Buga jerin sunayen wakilai, zai kasance ranar Alhamis, 13 ga Fabrairun 2025.

“Ranakun babban taron shiyoyin na Arewa maso Gabas, Kudu maso Gabas, da Kudu maso Kudu, zai kasance ranar Asabar, 22 ga Fabrairun 2025.

“Amincewa da babban taron shiyoyin, zai kasance ranar Talata, 25 ga Fabrairu, 2025.

“Babban taron shiyoyi na shiyyar Arewa ta Tsakiya da Kudu maso Yamma, zai gudana a ranar Asabar, 22 ga Maris, 2025. Amincewa da babban taron, zai kasance ranar Laraba, 26 ga Maris, 2025.”

Jam’iyyar ta bukaci duk masu son yin takara da su tuntubi sakatariyar jam’iyyar na kasa don samun bayanai kan kudaden da ake bukata da sauran tambayoyi.

Ologunagba ya kuma ja hankalin dukkan shugabannin PDP da masu ruwa da tsaki, da ’ya’yan jam’iyyar da su ci gaba da hada kan su, su kuma yi kokarin ganin jam’iyyar ta samu ci gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: PDPShiyoyyiSiyasaTaroZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kanana Da Matsakaitan Kamfanonin Sin Sun Samu Bunkasuwa Yadda Ya Kamata

Next Post

Nijeriya Ta Doke Kasar Libya A Akwa Ibom

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

5 days ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

6 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga ZaÉ“en Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

6 days ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

2 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
Nijeriya Ta Doke Kasar Libya A Akwa Ibom

Nijeriya Ta Doke Kasar Libya A Akwa Ibom

LABARAI MASU NASABA

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

July 31, 2025
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

2027: Ba Mu Kafa HaÉ—akarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC

July 31, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

July 31, 2025
Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

July 31, 2025
Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

July 31, 2025
Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.