• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin ziyarar da Nancy Pelosi ke shirin kai wa Taiwan ba Takala ba ce?

by CMG Hausa
3 years ago
Speaker of the House Nancy Pelosi, D-Calif., reacts to the Supreme Court decision overturning Roe v. Wade, at the Capitol in Washington, Friday, June 24, 2022. (AP Photo/J. Scott Applewhite)

Speaker of the House Nancy Pelosi, D-Calif., reacts to the Supreme Court decision overturning Roe v. Wade, at the Capitol in Washington, Friday, June 24, 2022. (AP Photo/J. Scott Applewhite)

Ko shakka babu, burin Amurka shi ne tada hankalin duniya domin cimma wani muradi nata na kashin kai. Kuma dukkan alamu sun nuna cewa, sam ba ta kaunar zaman lafiya.

A ranar Juma’ar da ta gabata, shugaban Amurka ya bayyana cewa, kasarsa na girmama manufar kasar Sin daya tak a duniya, kuma ba ta goyon bayan ’yancin kan yankin Taiwan.

Sai dai har kullum, Amurkar kan yi amai ne ta lashe. Yayin da shugaban kasar ya bayyana haka tare da cewa hadin gwiwar Sin da kasarsa na da muhimmanci ga zaman lafiyar duniya, sai kuma aka ji shugabar majalisar wakilan kasar Nancy Pelosi na shirin ziyartar yankin na Taiwan.

Wannan fa na zuwa ne bayan kasar Sin ta yi gargadi da babbar murya game da hakan. Har kullum, shugaban Amurka kan furta wani abu dake karfafa gwiwar alakar kasarsa da Sin za ta kyautata domin amfanin al’ummun duniya, amma kuma, sai ’yan siyasar kasar su furta ko aiwatar da wani abu da ya sabawa hakan. Shin babu fahimta ne tsakanin shugaban kasar Amurka da sauran ’yan siyasar kasar? Ko kuma wani salo ne na makircin Amurka?

Idan Amurkar ba ta sani ba, wannan yana kara zubar da kimarta ne a idon duniya. Domin a ranar Juma’a, duk da muhimman batutuwa da aka tabo, an yi tsammanin ganin kyautatuwar lamura da dangantaka tsakanin manyan kasashen biyu, amma kuma batun ziyarar Nancy Pelosi, ya kawar da wannan tunani.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

Duk inda Amurka ta shiga, ta tsoma baki cikin harkokinsu na gida, to ba a karewa lafiya. Ga misali nan na zahiri ana gani a kan Ukraine, lamarin da ba kasashen dake rikicin kawai ya shafa ba, har da na shiyyarsu da sauran nahiyoyi, kai da daukacin duniya.

Kasar Sin dai, ta yi gargadi game da rashin amincewarta da ziyarar ta Nancy Pelosi a yankin Taiwan. Taiwan, yanki ne mallakar kasar Sin, don hak duk wata hulda ta jakadanci ta kai tsaye da yankin, ya keta manufar Sin daya tak a duniya, da tubalin hadin gwiwar Sin da kowacce kasa, haka zalika, ya take dokokin huldar kasa da kasa. Bisa la’akari da hakan, duk wata alaka ta kai tsaye da yankin, abu daya yake nufi, wato takalar fada.

A bayyane yake cewa, burin Amurka shi ne kokarin ta da rikici a Sin, ta daidaita al’ummar kasar sama da biliyan 1.4 dake zaune lami lafiya, da hargitsa tattalin arzikinta da tasiri da ma karfinta a duniya, sannan za ta ja gefe ta bar Taiwan, hakarta ta cimma ruwa ke nan.
A nata bangare dai kasar Sin kamar kowacce kasa mai sanin ya kamata, burinta shi ne tabbatar da dunkulewar kasar cikin lumana, sai dai kuma, hakan ba ya nufin za ta kyale ana yadda aka ga dama da yankunanta. Ta kuma nanata cewa, za ta yi dukkan mai yuwuwa, ciki har da daukar matakan soji, domin kare cikakken ’yanci da iko da yankunanta.(Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Next Post
Kwamishinan Yobe, Goni Bukar, Ya Rasu A Hadarin Mota

Kwamishinan Yobe, Goni Bukar, Ya Rasu A Hadarin Mota

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.